< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
Vision d’Isaïe, fils d’Amos, qu’il a vue touchant Juda et Jérusalem, dans les jours d’Ozias, de Joathan, d’Achaz et d’Ezéchias, rois de Juda.
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
Ecoutez, cieux, et prête l’oreille, terre, parce que le Seigneur a parlé. J’ai nourri des fils et je les ai élevés, mais eux m’ont méprisé.
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
Un bœuf connaît son possesseur, un âne l’étable de son maître; mais Israël ne m’a pas connu, et mon peuple n’a pas eu d’intelligence.
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
Malheur à la nation pécheresse, au peuple chargé d’iniquité, à la race perverse, aux enfants scélérats; ils ont abandonné le Seigneur, ils ont blasphémé le saint d’Israël, ils sont retournés en arrière.
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
Où vous frapperai-je encore, vous qui ajoutez à la prévarication? toute tête est
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
De la plante des pieds jusqu’au sommet de la tête, rien en lui de sain; c’est blessure, meurtrissure, plaie enflammée, qui n’a été ni bandée, ni pansée, ni adoucie par l’huile.
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
Votre terre est déserte, vos cités brûlées par le feu; votre pays, devant vous, des étrangers le dévorent, et il sera désolé comme dans une dévastation de l’ennemi.
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
Et la fille de Sion sera laissée comme un berceau dans une vigne, comme une cabane dans un champ de concombres, comme une cité qui est livrée au pillage.
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
Si le Seigneur des armées ne nous avait réservé un rejeton, nous aurions été comme Sodome. Nous serions devenus semblables à Gomorrhe.
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
Écoutez la parole du Seigneur, princes de Sodome; prêtez l’oreille à la loi de notre Dieu, peuple de Gomorrhe.
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
Qu’ai-je à faire de la multitude de vos victimes? dit le Seigneur. Je suis rassasié; les holocaustes des béliers, et la graisse des animaux gras, et le sang des veaux et des agneaux et des boucs, je n’en veux point.
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
Lorsque vous êtes venus en ma présence, qui a demandé ces choses de vos mains, afin que vous vous promeniez dans mes parvis?
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
Ne m’offrez plus de sacrifice en vain; l’encens m’est en abomination. Ma néoménie, le sabbat et les autres fêtes, je ne les souffrirai point; vos assemblées sont iniques.
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
Vos calendes, et vos solennités, mon âme les hait: elles me sont devenues à charge; j’ai peine à les souffrir.
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
Et lorsque vous étendrez vos mains, je détournerai mes yeux de vous; lorsque vous multiplierez la prière, je n’exaucerai pas; car vos mains sont pleines de sang.
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
Lavez-vous, purifiez-vous, ôtez le mal de vos pensées de devant mes yeux; cessez d’agir avec perversité;
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
Apprenez à bien faire, cherchez la justice, venez au secours de l’opprimé, jugez l’orphelin, défendez la veuve.
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
Et venez, et accusez-moi, dit le Seigneur: si vos péchés sont comme l’écarlate, comme la neige ils deviendront blancs, et s’ils sont rouges comme le vermillon, comme la laine ils seront blancs.
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
Si vous voulez, et que vous m’écoutiez, vous mangerez les biens de la terre.
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
Que si vous ne voulez pas, et que vous me provoquiez au courroux, le glaive vous dévorera, parce que la bouche du Seigneur a parlé.
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
Comment est devenue une prostituée la cité fidèle et pleine de jugement? la justice a habité en elle, mais maintenant ce sont des meurtriers.
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
Ton argent s’est converti en scorie; ton vin a été mêlé d’eau.
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
Tes princes sont infidèles, compagnons de voleurs; tous aiment les présents et poursuivent les récompenses. Ils ne rendent pas justice à l’orphelin, et la cause de la veuve n’a pas d’accès auprès d’eux.
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
À cause de cela, dit le Seigneur Dieu des armées, le fort d’Israël: Ah! je me consolerai sur mes ennemis, je me vengerai de ceux qui me sont opposés.
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
Et je tournerai ma main vers toi, et j’épurerai par le feu tes scories, et j’enlèverai l’alliage qui est en toi.
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
Et je rétablirai tes juges comme ils furent d’abord, et tes conseillers comme anciennement; après cela tu seras appelée la cité du juste, ville fidèle.
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
Sion, par le jugement, sera rachetée, et on la ramènera par la justice;
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
Et le Seigneur brisera les scélérats et les pécheurs tous ensemble; et ceux qui ont abandonné le Seigneur seront consumés.
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
Car ils seront confondus par les idoles auxquelles ils ont sacrifié; et vous rougirez des jardins que vous aviez choisis,
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
Lorsque vous serez comme un chêne dont les feuilles tombent et comme un jardin sans eau.
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
Et votre force sera comme la cendre chaude de l’étoupe, et votre œuvre comme une étincelle; et ils s’embraseront l’un et l’autre ensemble, et il n’y aura personne qui l’éteigne.

< Ishaya 1 >