< Hosiya 1 >
1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
Parole du Seigneur qui fut adressée à Osée, fils de Bééri, dans les jours d’Ozias, de Joathan, d’Achaz et d’Ezéchias, rois de Juda, et dans les jours de Jéroboam, fils de Joas, roi d’Israël.
2 Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
Commencement des paroles du Seigneur par Osée; et le Seigneur dit à Osée: Va, prends pour toi une femme de fornications, et des enfants de fornications; parce que forniquant la terre forniquera en se séparant du Seigneur.
3 Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
Et il alla, et il prit Gomer, fille de Débelaïm; et elle conçut, et elle lui enfanta un fils.
4 Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
Et le Seigneur dit à Osée: Appelle son nom Jezrahel; parce qu’encore un peu de temps, et je visiterai le sang de Jezrahel sur la maison de Jéhu, et je ferai cesser le royaume de la maison d’Israël.
5 A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
Et en ce jour-là, je briserai l’arc d’Israël dans la vallée de Jezrahel.
6 Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
Et elle conçut encore, et elle enfanta une fille. Et le Seigneur dit à Osée: Appelle son nom, Sans miséricorde; parce qu’à l’avenir je n’aurai plus de pitié pour la maison d’Israël, mais que je les oublierai entièrement.
7 Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
Et j’aurai pitié de la maison de Juda, et je les sauverai par le Seigneur leur Dieu, et je ne les sauverai pas par l’arc, par le glaive, et par la guerre, et par les chevaux et par les cavaliers.
8 Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
Et Gomer sevra sa fille qui était appelée Sans miséricorde. Et elle conçut et elle enfanta un fils.
9 Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
Et Dieu dit: Appelle son nom, Non mon peuple, parce que vous n’êtes plus mon peuple, et que moi je ne serai pas pour vous.
10 “Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
Et le nombre des enfants d’Israël sera comme le sable de la mer, qui est sans mesure, et qui ne se comptera pas, et dans le lieu où il leur sera dit: Vous n’êtes pas mon peuple, il leur sera dit: Vous êtes les fils du Dieu vivant.
11 Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.
Et les fils de Juda et les fils d’Israël se réuniront ensemble; et ils se donneront un seul chef, et ils s’élèveront de la terre, parce que grand est le jour de Jezrahel.