< Hosiya 1 >

1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
La parole de l'Éternel qui fut adressée à Osée, fils de Beéri, dans le temps de Hosias, de Jotham, d'Achaz, d'Ézéchias, rois de Juda, et dans le temps de Jéroboam, fils de Joas, roi d'Israël.
2 Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
Quand l'Éternel commença à parler à Osée, l'Éternel dit à Osée: Va, prends-toi une femme impure et des enfants impurs, car le pays pour se livrer à l'impureté quitte l'Éternel.
3 Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
Et il alla, et prit Gomer, fille de Diblaïm; et elle devint enceinte et lui enfanta un fils.
4 Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
Et l'Éternel lui dit: Appelle-le du nom de Jizréel, car encore un peu de temps et je vengerai sur la maison de Jéhu le sang versé à Jizréel, et je mettrai fin au royaume de la maison d'Israël.
5 A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
Et il arrivera dans ce jour-là que je briserai l'arc d'Israël dans la vallée de Jizréel.
6 Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
Et elle devint encore enceinte, et enfanta une fille. Et Il lui dit: Appelle-la du nom de Disgraciée, car désormais je ne donnerai plus ma grâce à la maison d'Israël, pour lui pardonner.
7 Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
Mais à la maison de Juda je veux donner ma grâce, et la sauver par l'Éternel, son Dieu, et je ne la sauverai ni par l'arc, ni par l'épée, ni par la guerre, ni par les chevaux, ni par la cavalerie.
8 Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
Et elle sevra Disgraciée, et elle conçut et enfanta un fils.
9 Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
Et Il dit: Appelle-le du nom de Tu-n'es-pas-mon-peuple; car vous n'êtes pas mon peuple, et moi je ne suis plus à vous.
10 “Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
Mais elle ne reconnaît pas que c'est moi qui lui ai donné le blé et le moût et l'huile, et en abondance l'argent et l'or dont ils ont fait un Baal.
11 Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.
Aussi je retirerai mon blé dans sa saison et mon moût à son époque, et reprendrai ma laine et mon lin, couverture de sa nudité.

< Hosiya 1 >