< Hosiya 1 >

1 Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
Parole de Yahweh qui fut adressée à Osée, fils de Béeri, dans les jours d'Ozias, de Joatham, d'Achaz, d'Ezéchias, rois de Juda, et dans les jours de Jéroboam, fils de Joas, roi d'Israël.
2 Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
Lorsque Yahweh commença à parler à Osée, Yahweh dit à Osée: " Va, prends une femme de prostitution et des enfants de prostitution, car le pays ne fait que se prostituer en abandonnant Yahweh. "
3 Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
Il alla et prit Gomer, fille de Débelaïm; elle conçut et lui enfanta un fils.
4 Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
Et Yahweh lui dit: " Nomme-le Jezrahel, car encore un peu de temps et je punirai le sang de Jezrahel sur la maison de Jéhu, et je mettrai fin à la royauté de la maison d'Israël.
5 A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
En ce jour-là je briserai l'arc d'Israël dans la plaine de Jezrahel. "
6 Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
Elle conçut encore et enfanta une fille; et Yahweh dit à Osée: " Nomme-la Lô-Ruchama, car je n'aurai plus compassion de la maison d'Israël pour lui pardonner ses péchés.
7 Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
Mais j'aurai compassion de la maison de Juda, et je les sauverai par Yahweh, leur Dieu; je ne les sauverai ni par l'arc et l'épée, ni par le combat, ni par les chevaux et les cavaliers. "
8 Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
Elle sevra Lô-Ruchama; puis elle conçut et enfanta un fils.
9 Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
Et Yahweh dit à Osée: " Nomme-le Lô-Ammi, car vous n'êtes pas mon peuple, et moi je ne serai pas votre Dieu. "
10 “Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
Le nombre des enfants d'Israël sera comme le sable de la mer, qui ne se mesure, ni ne se compte; et au lieu où on leur disait: " Vous n'êtes pas mon peuple, " on leur dira: " Fils du Dieu vivant!
11 Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.
Et les enfants de Juda et les enfants d'Israël se réuniront, ils se donneront un même chef et monteront hors du pays, car grande sera la journée de Jezrahel.

< Hosiya 1 >