< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
No te alegres, Israel, hasta el júbilo como las naciones; porque fuisteis infieles a vuestro Dios. Amas el salario de una prostituta en cada trilla de grano.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
La era y el lagar no los alimentarán, y el vino nuevo le fallará.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
No habrán de habitar en la tierra de Yahvé; pero Efraín volverá a Egipto, y comerán alimentos impuros en Asiria.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
No derramarán ofrendas de vino a Yahvé, ni le serán agradables. Sus sacrificios serán para ellos como el pan de los dolientes; todos los que coman de ella serán contaminados; porque su pan será para su apetito. No entrará en la casa de Yahvé.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
¿Qué harás en el día de la asamblea solemne, y en el día de la fiesta de Yahvé?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Porque, he aquí, cuando huyen de la destrucción, Egipto los reunirá. Memphis los enterrará. Las ortigas poseerán sus agradables cosas de plata. Las espinas estarán en sus tiendas.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Han llegado los días de la visita. Han llegado los días del ajuste de cuentas. Israel considerará al profeta como un tonto, y el hombre que se inspira en la locura, por la abundancia de tus pecados, y porque su hostilidad es grande.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
Un profeta vela por Efraín con mi Dios. La trampa del cazador está en todos sus caminos, y la hostilidad en la casa de su Dios.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Se han corrompido profundamente, como en los días de Gabaa. Se acordará de su iniquidad. Los castigará por sus pecados.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
Encontré a Israel como uvas en el desierto. Vi a tus padres como la primera maduración de la higuera en su primera temporada; pero vinieron a Baal Peor, y se consagraron a la cosa vergonzosa, y se volvieron abominables como lo que amaban.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
En cuanto a Efraín, su gloria volará como un pájaro. No habrá nacimientos, ni niños, ni concepción.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Aunque crian a sus hijos, pero los despojaré, de modo que no quede ni un solo hombre. En efecto, ¡ay de ellos también cuando me alejo de ellos!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
He visto a Efraín, como Tiro, plantado en un lugar agradable; pero Efraín sacará a sus hijos al asesino.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Dales, Yahvé, ¿qué vas a dar? Dales un vientre de aborto y pechos secos.
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
“Toda su maldad está en Gilgal; porque allí los odiaba. A causa de la maldad de sus actos, los expulsaré de mi casa. No los amaré más. Todos sus príncipes son rebeldes.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Efraín es golpeado. Su raíz se ha secado. No darán ningún fruto. Aunque den a luz, mataré a los seres queridos de su vientre”.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Mi Dios los expulsará, porque no le hicieron caso; y serán errantes entre las naciones.

< Hosiya 9 >