< Hosiya 9 >
1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Ne raduj se, Izrailju, veseleæi se kao narodi, što se kurvaš otstupivši od Boga svojega, miluješ platu kurvarsku po svijem gumnima žitnijem.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
Gumno i kaca neæe ih hraniti, i mast æe ih prevariti.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
Oni neæe nastavati u zemlji Gospodnjoj; nego æe se vratiti Jefrem u Misir, i oni æe jesti neèistotu u Asirskoj.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
Neæe prinositi Gospodu vina, niti æe mu biti ugodne žrtve njihove, nego æe im biti kao hljeb onijeh koji tuže, ko ga god jede oskvrniæe se, jer im je hljeb za žrtve njihove, neæe uæi u dom Gospodnji.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
Šta æete èiniti na dan svetkovine i na dan praznika Gospodnjega?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Jer gle, otiæi æe pustošenja radi; Misir æe ih pribrati, Memfis æe ih pogrepsti; zaklade njihove od srebra naslijediæe kopriva, trnje æe im biti u šatorima.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Doðoše dani pohoðenju, doðoše dani plaæanju; poznaæe Izrailj; proroci su ludi, bezumni su u kojima je duh, za mnoštvo bezakonja tvojega i veliku mržnju.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
Stražar je Jefremov s Bogom mojim, prorok je zamka ptièarska po svijem putovima njegovijem, mržnja je u domu Boga njegova.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Duboko su se pokvarili kao u vrijeme Gavajsko; opomenuæe se bezakonja njihova, i pohodiæe grijehe njihove.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
Naðoh Izrailja kao grožðe u pustinji; vidjeh oce vaše kao prve smokve na drvetu u poèetku njegovu; oni otidoše k Velfegoru, i odvojiše se za sramotom, i postaše gadni kako im bješe milo.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
Jefremova æe slava odletjeti kao ptica od roðenja i od utrobe i od zaèetka.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Ako li i othrani sinove svoje, ja æu ih uèiniti da budu bez djece, da ne ostane nijedan; i teško njima kad otstupim od njih.
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Jefrem, kad ga gledah, bješe kao Tir, posaðen na ljupku mjestu; ali æe Jefrem izvesti krvniku sinove svoje.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Podaj im, Gospode; šta æeš im dati? podaj im utrobu pometljivu i dojke usahle.
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
Sva je zloæa njihova u Galgalu; zato ondje mrzim na njih; za zloæu djela njihovijeh izagnaæu ih iz doma svojega; neæu ih više ljubiti: svi su knezovi njihovi odmetnici.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Udaren bi Jefrem; korijen im posahnu, neæe roditi roda; ako i rode, ubiæu mili porod utrobe njihove.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Odbaciæe ih Bog moj, jer ga ne slušaju, i skitaæe se po narodima.