< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Não se regozije, Israel, para regozijar-se como as nações; pois você foi infiel a seu Deus. Você adora o salário de uma prostituta em cada eira de grãos.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
A eira e o lagar não os alimentam, e o novo vinho lhe falhará.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
Eles não vão morar na terra de Yahweh; mas Efraim voltará ao Egito, e eles comerão alimentos impuros na Assíria.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
Eles não vão derramar ofertas de vinho para Yahweh, nem serão agradáveis a ele. Seus sacrifícios serão para eles como o pão das carpideiras; todos que comerem dele serão poluídos; para seu pão será para seu apetite. Ela não entrará na casa de Yahweh.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
O que você fará no dia da assembléia solene, e no dia da festa de Yahweh?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Pois, eis que quando eles fogem da destruição, O Egito irá reuni-los. Memphis vai enterrá-los. As urtigas possuirão suas coisas agradáveis de prata. Os espinhos estarão em suas tendas.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Os dias da visitação chegaram. Chegaram os dias do acerto de contas. Israel considerará o profeta como sendo um tolo, e o homem que está inspirado a ser insano, por causa da abundância de seus pecados, e porque sua hostilidade é grande.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
Um profeta vigia Efraim com meu Deus. A armadilha de um caçador de aves está em todos os seus caminhos, e hostilidade na casa de seu Deus.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Eles se corromperam profundamente, como nos dias de Gibeah. Ele se lembrará de sua iniqüidade. Ele vai puni-los por seus pecados.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
Encontrei Israel como uvas no deserto. Eu vi seus pais como os primeiros maduros na figueira em sua primeira estação; mas eles vieram para Baal Peor, e se consagraram ao vergonhoso, e se tornaram abomináveis como aquilo que eles amavam.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
As para Efraim, sua glória voará para longe como um pássaro. Não haverá nascimento, ninguém com filhos e nenhuma concepção.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Embora eles criem seus filhos, no entanto, eu os desmarcarei, para que não fique um homem. De fato, ai deles também quando eu me afasto deles!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Eu vi o Ephraim, como o Tyre, plantado em um lugar agradável; mas Efraim levará seus filhos até o assassino.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Dê a eles - Yahweh o que você vai dar? Dê-lhes um ventre abortado e seios secos.
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
“Toda sua maldade está em Gilgal; pois lá eu os odiava. Por causa da maldade de seus atos, eu os expulsarei de minha casa! Eu não vou amá-los mais. Todos os seus príncipes são rebeldes.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Ephraim é atingido. Sua raiz secou. Eles não darão frutos. Ainda que eles dêem à luz, ainda assim matarei os amados de seu ventre”.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Meu Deus os rejeitará, porque eles não o escutaram; e eles serão viajantes entre as nações.

< Hosiya 9 >