< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Nepriecājies, Israēl, ar gavilēšanu kā tās tautas, jo tu dzen maucību, atkāpdamies no sava Dieva, tu mīļo mauku algu uz visiem labības kloniem.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
Klons un eļļas spaids viņus nemielos un jaunais vīns tos pievils.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
Tie nepaliks Tā Kunga zemē, bet Efraīms griezīsies atpakaļ uz Ēģipti, un Asīrijā tie ēdīs nešķīstu.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
Tie Tam Kungam nenesīs dzeramus upurus no vīna, un viņu kaujamie upuri viņam nepatiks; tie viņiem būs kā bēru maize. Visi, kas to ēd, apgānās, jo viņu maize ir priekš viņiem pašiem, un nenāk Tā Kunga namā.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
Ko tad jūs darīsiet svētkos un Tā Kunga svētā dienā?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Jo redzi, tiem jāaiziet tā posta dēļ, Ēģipte tos sapulcinās, Memfisa viņus apraks. Nātres mantos viņu sudraba dārgumus, ērkšķi būs viņu dzīvokļos.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Piemeklēšanas dienas nākušas, atmaksāšanas dienas ir klāt, Israēls to samanīs! Tie pravieši ir ģeķi, tie gara vīri ir traki, - visa tava lielā nozieguma un lielā naida dēļ.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
Efraīms lūko manam Dievam garām, un pravieši ir palikuši par slazda valgiem uz visiem viņa ceļiem, naids ir viņu dieva namā.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Tie ir dziļi maitājušies tā kā Ģibejas dienās; viņš pieminēs viņu noziegumu, viņš piemeklēs viņu grēkus.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
Es atradu Israēli kā vīna ogu ķekarus tuksnesī, Es ieraudzīju jūsu tēvus kā pirmajus augļus pie vīģes koka; bet tie nogāja pie BaālPeora un padevās tam bezkaunīgam un tapa tik neganti kā viņu drauģeļi.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
Efraīma godība aizskries kā putns, ka tur ne dzemdēs, nedz taps grūtas, nedz ieņems.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Un jebšu tie savus bērnus uzaudzinātu, tomēr Es tiem tos gribu laupīt, ka cilvēku neatliek. Ak vai, tiem, kad Es no tiem būšu atstājies!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Efraīms, ko Es biju izredzējis, būt par Tiru, bija stādīts skaistā vietā, bet Efraīmam savi bērni jaiznes slepkavam.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Dod tiem, ak Kungs! Ko lai Tu dodi? Dod tiem neauglīgas miesas un izsīkušas krūtis.
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
Visa viņu negantība ir Gilgalā, tur Es tos ienīdēju. Viņu ļauno darbu dēļ Es tos izdzīšu no Sava nama, Es joprojām tos vairs nemīļošu; - visi viņu lielkungi ir atkāpēji.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Efraīms ir sasists, viņu sakne ir izkaltusi; tie nenesīs nekādus augļus; un jebšu tie dzemdinātu, tomēr Es viņu miesas mīlulīšus gribu nokaut.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Mans Dievs tos atmetīs, tāpēc ka tie Viņam neklausīja, un tie būs bēguļi starp tautām.

< Hosiya 9 >