< Hosiya 9 >
1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Ne te réjouis pas, Israël, jusqu'à l'allégresse, comme les autres peuples; car tu es adultère, tu désertes ton Dieu; car tu aimes à recevoir le salaire de l'impudicité sur toutes les aires à blé.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
Ni aire, ni pressoir ne les nourrira, et le moût trompera leur attente.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
Ils ne resteront pas dans le pays de l'Éternel; Éphraïm doit retourner en Egypte, et manger en Assyrie des aliments immondes.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
Ils ne feront plus à l'Éternel des libations de vin, et leurs victimes ne lui seront plus agréables; elles seront pour eux comme le pain du deuil: quiconque en mange se souille; car leur pain ne sera que pour eux, et n'entrera point dans la maison de l'Éternel.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
Que ferez-vous aux jours solennels, et aux jours des fêtes de l'Éternel?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Car voici, ils vont émigrer de leur pays dévasté, l'Egypte les recueillera, Memphis leur donnera la sépulture. De tout ce qu'ils ont de précieux en argent les orties s'empareront, et les ronces seront dans leurs cabanes.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Ils arrivent les jours du châtiment, ils arrivent les jours de la rétribution! Israël le saura! Le prophète est en démence, [dites-vous, ] l'homme inspiré en délire! C'est à cause de la grandeur de ton crime et de tous les actes odieux.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
Éphraïm est aux aguets contre mon Dieu; le prophète rencontre un filet d'oiseleur sur toutes ses voies, la haine [le poursuit] dans la maison de son Dieu.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Profonde est leur corruption; comme aux jours de Guibha. Il se souviendra de leur crime, châtiera leurs péchés.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
Je trouvai Israël comme des raisins dans le désert, je vis vos pères de l'œil dont on regarde des primeurs sur un figuier qui donne ses premiers fruits; mais eux ils allèrent à Baal-Péhor, et se vouèrent à l'infamie et devinrent abominables comme leurs amours.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
Comme un oiseau s'envolera la gloire d'Éphraïm; plus de naissances, plus de grossesses, plus de conception.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Quand même ils élèveraient des fils, je les ferai être sans enfants, pour qu'il n'y ait plus d'hommes. Oui, malheur à eux-mêmes, quand je m'éloignerai d'eux!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Éphraïm, aussi loin que porte ma vue jusqu'à Tyr, est planté dans une campagne fertile, et les fils d'Éphraïm en seront tirés et livrés au meurtrier.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Donne-leur, ô Éternel!… que leur donneras-tu?… donne-leur un sein qui avorte et des mamelles arides.
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
Toute leur méchanceté [se montre] à Guilgal; oui, là, ils me sont odieux par la malice de leurs actions; de ma maison je les chasserai, et n'aurai plus d'amour pour eux; tous leurs chefs sont réfractaires.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Éphraïm est frappé; sa racine sèche; ils ne porteront plus de fruit; quand même ils auront des enfants, je ferai périr le doux fruit de leur sein.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Mon Dieu les rejettera, parce qu'ils ne lui sont pas obéissants, et ils seront fugitifs parmi les peuples.