< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Israël ne te réjouis point jusqu'à t'égayer comme les [autres] peuples, de ce que tu as commis adultère, [te retirant] loin de ton Dieu. Tu as aimé le salaire [de la fornication] dans toutes les aires de froment.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
L'aire et la cuve ne les repaîtra point, et le vin doux leur mentira.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
Ils ne demeureront point en la terre de l'Eternel, mais Ephraïm retournera en Egypte, et ils mangeront en Assyrie la viande souillée.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
Ils ne feront point aspersion de vin à l'Eternel, et leurs sacrifices ne lui plairont point; [mais ils] leur seront comme le pain de deuil; tous ceux qui en mangeront seront souillés; parce que leur pain est pour leurs trépassés, il n'entrera point dans la maison de l'Eternel.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
Que ferez-vous aux jours des fêtes solennelles, et aux jours des fêtes de l'Eternel?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Car voici, ils s'en sont allés à cause du dégât; l'Egypte les serrera, Memphis les ensevelira; on ne désirera que leur argent; le chardon sera leur héritier, et l'épine sera dans leurs tabernacles.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Les jours de la visitation sont venus, les jours de la rétribution sont venus, et Israël le saura. Les Prophètes sont fous, les hommes de révélation sont insensés à cause de la grandeur de ton iniquité, et de [ta] grande aversion.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
La sentinelle d'Ephraïm est avec mon Dieu; [mais] le Prophète est un filet d'oiseleur dans tous les chemins d'Ephraïm, il [est] l'aversion contre la maison de son Dieu.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Ils se sont extrêmement corrompus, comme aux jours de Guibha; il se souviendra de leur iniquité, il punira leurs péchés.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
J'avais, [dira-t-il], trouvé Israël comme des grappes dans un désert; j'avais vu vos pères comme un premier fruit en un figuier dans son commencement; [mais] ils sont entrés vers Bahal-péhor, et se sont séparés pour aller après une chose honteuse, et se sont rendus abominables comme ce qu'ils ont aimé.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
La gloire d'Ephraïm s'envolera aussi vite qu'un oiseau, dès la naissance, dès le ventre, et dès la conception.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Que s'ils élèvent leurs enfants, je les en priverai, [tellement que pas un d'entre eux] ne deviendra homme; car aussi, malheur à eux, quand je me serai retiré d'eux.
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Ephraïm était comme j'ai vu Tyr, plantée en un lieu agréable, mais néanmoins Ephraïm mènera ses fils au meurtrier.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Ô Eternel! donne-leur; [mais] que leur donnerais-tu? donne-leur un sein sujet à avorter, et des mamelles taries.
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
Toute leur méchanceté est à Guilgal; c'est pourquoi je les ai là haïs; je les chasserai de ma maison à cause de la malice de leurs actions; je ne continuerai plus à les aimer; tous les principaux d'entre eux sont revêches.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Ephraïm a été frappé; et leur racine est asséchée, ils ne feront plus de fruit; et s'ils engendrent [des enfants], je mettrai à mort les [fruits] désirables de leur ventre.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Mon Dieu les rejettera, parce qu'ils ne l'ont point écouté, et ils seront vagabonds parmi les nations.

< Hosiya 9 >