< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Israël, ne te livre pas à la joie, à l’allégresse, comme les peuples, De ce que tu t’es prostitué en abandonnant l’Éternel, De ce que tu as aimé un salaire impur dans toutes les aires à blé!
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
L’aire et le pressoir ne les nourriront pas, Et le moût leur fera défaut.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
Ils ne resteront pas dans le pays de l’Éternel; Éphraïm retournera en Égypte, Et ils mangeront en Assyrie des aliments impurs.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
Ils ne feront pas à l’Éternel des libations de vin: Elles ne lui seraient point agréables. Leurs sacrifices seront pour eux comme un pain de deuil; Tous ceux qui en mangeront se rendront impurs; Car leur pain ne sera que pour eux, Il n’entrera point dans la maison de l’Éternel.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
Que ferez-vous aux jours solennels, Aux jours des fêtes de l’Éternel?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
Car voici, ils partent à cause de la dévastation; L’Égypte les recueillera, Moph leur donnera des sépulcres; Ce qu’ils ont de précieux, leur argent, sera la proie des ronces, Et les épines croîtront dans leurs tentes.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
Ils arrivent, les jours du châtiment, Ils arrivent, les jours de la rétribution: Israël va l’éprouver! Le prophète est fou, l’homme inspiré a le délire, A cause de la grandeur de tes iniquités et de tes rébellions.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
Éphraïm est une sentinelle contre mon Dieu; Le prophète… un filet d’oiseleur est sur toutes ses voies, Un ennemi dans la maison de son Dieu.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
Ils sont plongés dans la corruption, comme aux jours de Guibea; L’Éternel se souviendra de leur iniquité, Il punira leurs péchés.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
J’ai trouvé Israël comme des raisins dans le désert, J’ai vu vos pères comme les premiers fruits d’un figuier; Mais ils sont allés vers Baal-Peor, Ils se sont consacrés à l’infâme idole, Et ils sont devenus abominables comme l’objet de leur amour.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
La gloire d’Éphraïm s’envolera comme un oiseau: Plus de naissance, plus de grossesse, plus de conception.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
S’ils élèvent leurs enfants, Je les en priverai avant qu’ils soient des hommes; Et malheur à eux, quand je les abandonnerai!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
Éphraïm, aussi loin que portent mes regards du côté de Tyr, Est planté dans un lieu agréable; Mais Éphraïm mènera ses enfants vers celui qui les tuera.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Donne-leur, ô Éternel!… Que leur donneras-tu?… Donne-leur un sein qui avorte et des mamelles desséchées!
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
Toute leur méchanceté se montre à Guilgal; C’est là que je les ai pris en aversion. A cause de la malice de leurs œuvres, Je les chasserai de ma maison. Je ne les aimerai plus; Tous leurs chefs sont des rebelles.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Éphraïm est frappé, sa racine est devenue sèche; Ils ne porteront plus de fruit; Et s’ils ont des enfants, Je ferai périr les objets de leur tendresse.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
Mon Dieu les rejettera, parce qu’ils ne l’ont pas écouté, Et ils seront errants parmi les nations.

< Hosiya 9 >