< Hosiya 9 >

1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
[You people of] Israel, do not shout joyfully [during your festivals] like [people of other] nations do! [I say that] because you have (not been faithful to/abandoned) me, your God. At every place where the people thresh grain you have [presented gifts to your idols like men] pay money to prostitutes.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
[But soon] there will not be enough grain [MTY, PRS] and wine [MTY, PRS] for you.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
And you people will not remain in the land that I, Yahweh, [gave to your ancestors]. You will be [captured and] taken to [Assyria], [where you will become slaves like your ancestors were] in Egypt; and in Assyria you will be forced to eat food that Yahweh has forbidden you to eat.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
You Israelis will not [be able to] give wine offerings to him, or bring sacrifices to him. None of your other sacrifices will please him; they will be unacceptable to him, like [SIM] food that is touched by people at funerals, and everyone who eats that food will become unacceptable to him. They will be permitted to eat that food themselves, but they will not [be permitted to] bring it into the temple.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
At that time you will not [RHQ] be able to celebrate the feasts and sacred festivals.
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
And even if you escape and are not killed [by the Assyrians], you will be captured by [the army of] Egypt, and you will [die and] be buried in Memphis, [the capital of Egypt]. Briers will [grow up and] cover your treasures of silver, and thorns will grow in your [ruined] tents/houses.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
It is now the time for Yahweh to punish you, to pay you back for all the sins that you have committed. You people will [soon] know that. You have [committed] very many sins, and you very much hate Yahweh. You consider that the prophets are foolish, and you think that those who proclaim messages from him are crazy.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
My God appointed [me and the other] prophets to be [like] [MET] watchmen [to warn] you people of Israel, but everywhere that we go, [it is as though] people set traps for us and people are hostile [to us, even] in the temple of our God.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
The sins that the Israeli people have committed are as awful as [what the men of] Gibeah did long ago; [so] God will not forget the wicked things that they have done; he will punish the Israelis for [all] those sins.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
[Yahweh says], “When I first started [to do things to help] Israel, it seemed to me as though [SIM] I had found grapes in the desert. Your ancestors were [delightful], like [SIM] the first figs that grow on fig trees [each year]. But when they came to Peor [Mountain], they worshiped that disgusting idol Baal, and they became as disgusting as the idol that they loved.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
The things that cause Israel to be great will disappear like [SIM] a bird that flies away; [most of their women will] not become pregnant [DOU] or give birth to children.
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Even if their children are born and start to grow up, I will cause all of them to die [while they are still young]. Terrible things will happen to them when I abandon them!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
I have seen Israel become beautiful and prosperous like Tyre [city] was [before it was destroyed], but now the people of Israel will [be forced to] take their children to be slaughtered [by their enemies].”
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Yahweh, [I do not know] [RHQ] what I should ask for my people. So I ask that you do this one thing: Cause the women who are pregnant to have miscarriages and unable [to nurse their babies].
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
[Yahweh says], “Because of all the wicked things that my people did at Gilgal, that is where I started to hate them. [And now], because of [all] the sinful things that they have done, I will expel them from my country. I will not love them any longer; all their leaders rebel [against me].
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Israel is like [MET] a grapevine that is dried up; [like a vine] [MET] whose roots are withered and that produces no fruit. Even if the [women of Israel] give birth to [more] children, I will cause those children, whom they love, to die.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
The people of Israel have not obeyed me, their God, so I will reject them. [As a result], they will wander among the [other] nations, [searching for a place to live].”

< Hosiya 9 >