< Hosiya 9 >
1 Kada ku yi farin ciki, ya Isra’ila; kada ku yi murna kamar waɗansu al’ummai. Gama kun yi rashin aminci ga Allahnku; kuna son hakkokin karuwa a kowace masussuka.
Rejoice not, O Israel, Exult not, like the nations! For thou committest fornication, forsaking thy God! Thou lovest hire on every corn-floor.
2 Masussukai da wuraren matsin inabi ba za su ciyar da mutane ba; sabon ruwan inabi zai kāsa musu.
The floor and the vat shall not feed them, And the new wine shall deceive them.
3 Ba za su ci gaba da zama a ƙasar Ubangiji ba; Efraim zai koma Masar yă kuma ci abinci marar tsarki a Assuriya.
They shall not dwell in the land of Jehovah; To Egypt shall Ephraim go back, And eat unclean things in Assyria.
4 Ba za su zuba hadayun ruwan inabi ga Ubangiji ba, ba kuwa hadayunsu za su gamshe shi ba. Irin hadayun nan za su zama musu kamar burodin masu makoki; duk wanda ya ci su zai ƙazantu. Wannan abincin zai zama na kansu ne; ba zai zo cikin haikalin Ubangiji ba.
They shall pour out no offerings of wine to Jehovah, Nor shall their sacrifices please him; They shall be to them as the bread of mourners; All that eat thereof shall be polluted. Their bread shall be for their own hunger; It shall not come into the house of Jehovah.
5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar bukukkuwarku, a ranakun bikin Ubangiji?
What will ye do in the festal day, In the day of the feast of Jehovah?
6 Ko da sun kuɓuta daga hallaka, Masar za tă tattara su, Memfis kuma za tă binne su. Sarƙaƙƙiya za tă mamaye kayan azurfansu, ƙayayyuwa su tsiro a cikin tentunansu.
For, behold, they go forth from a wasted land; Egypt shall gather them; Memphis shall bury them; The precious places of their silver, Nettles shall possess them; Thorns shall spring up in their habitations.
7 Kwanakin hukunci suna zuwa, kwanakin ba da lissafi suna a kusa. Bari Isra’ila su san da wannan. Saboda zunubanku sun yi yawa ƙiyayyarku kuma ta yi yawa, har ake ɗauka annabi wawa ne, mutumin da aka iza kuwa mahaukaci.
The days of visitation are come; The days of retribution are come— Israel shall know that the prophet was foolish, That the man of the spirit was mad— For the greatness of` thy iniquity, and thy great hatred.
8 Annabi, tare da Allahna, su ne masu tsaro a bisa Efraim, duk da haka tarko na jiransa a dukan hanyoyi, da kuma ƙiyayya a cikin gidan Allahnsa.
If Ephraim seek an answer from my God, The prophet is as the snare of the fowler in all his ways, A net in the house of his God.
9 Sun nutse da zurfi cikin lalaci, kamar a kwanakin Gibeya. Allah zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta su saboda zunubansu.
They have deeply corrupted themselves, as in the days of Gibeah; He will remember their iniquity; He will requite their sins.
10 “Sa’ad da na sami Isra’ila, ya zama kamar samun inabi a hamada; sa’ad da na ga kakanninku, ya zama kamar ganin’ya’yan itace na farko a itacen ɓaure. Amma sa’ad da suka zo Ba’al-Feyor, suka keɓe kansu wa gumaka bankunya sai suka zama abubuwan banƙyama kamar abubuwan da suke ƙauna.
I found Israel as grapes in the wilderness; As the early fruit on the fig-tree, at its first time of bearing, I saw your fathers. But they went to Baal Peor, And separated themselves to shame, And had abominable idols according to their love.
11 Darajar Efraim za tă yi firiya tă tafi kamar tsuntsu, ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki.
The glory of Ephraim shall fly away as a bird; They shall not bring forth, nor bear in the womb, nor conceive;
12 Ko da sun yi renon’ya’ya, zan sa su yi baƙin cikin kowannensu. Kaitonsu sa’ad da na juya musu baya!
Yea, if they bring up children, I will utterly bereave them; Yea, woe to them when I depart from them!
13 Na ga Efraim, kamar birnin Taya, da aka kafa a wuri mai daɗi. Amma Efraim zai fitar da’ya’yansu ga masu yanka.”
I have seen Ephraim planted, like Tyre, in a rich pasture, Yet shall Ephraim bring out his children to the murderer.
14 Ka ba su, ya Ubangiji Me za ka ba su? Ka ba su mahaifar da za su yi ɓarin ciki da busassun nono.
Give them, O Jehovah! What wilt thou give them? Give them a miscarrying womb, And dry breasts!
15 “Saboda dukan muguntarsu a Gilgal, na ƙi su a can. Saboda ayyukansu na zunubi, zan kore su daga gidana. Ba zan ƙara ƙaunace su ba; dukan shugabanninsu’yan tawaye ne.
All their wickedness is in Gilgal; Yea, there have I hated them for the wickedness of their doings; I will drive them from my house; I will love them no more; All their princes are revolters.
16 An ka da Efraim, saiwarsu ta bushe, ba sa ba da amfani. Ko da sun haifi’ya’ya zan kashe waɗanda suka fi ƙauna.”
Ephraim is smitten; Their root is dried up; they shall bear no fruit; Yea, though they should beget children, I will destroy the beloved fruit of the womb.
17 Allahna zai ƙi su saboda ba su yi masa biyayya ba; za su zama masu yawo a cikin al’ummai.
My God shall cast them away, Because they have not hearkened to him, And they shall be wanderers among the nations.