< Hosiya 8 >

1 “Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
“Boru çalmaya hazırlan! Düşman kartal gibi dolaşıyor evimin üzerinde; Çünkü İsrail antlaşmaya uymadı, Yasama karşı çıktılar.
2 Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
‘Ey Tanrımız, Biz İsrailliler seni tanıyoruz!’ Diye bana yakarıyorlar.
3 Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
İyi olanı reddettiler, Düşman kovalayacak onları.
4 Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
Krallar atadılar bana sormadan, Önderler seçtiler benden habersiz. Altın ve gümüşleriyle yıkımlarına yol açan putlar yaptılar.
5 Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
Ey Samiriye, atın buzağı putunuzu, Öfkem alevleniyor size karşı! Hiç mi temiz olamayacaksınız?
6 Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
Çünkü bu İsrail'in işidir. O buzağıyı bir usta yaptı, Tanrı değildir o. Samiriye'nin buzağı putu parçalanacak.
7 “Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
Çünkü rüzgar eken kasırga biçer. Baş vermeyen buğday un vermez. Verse bile yabancılar yutacak onu.
8 An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
“Yutuldu İsrail, Şimdi uluslar arasında kimsenin beğenmediği bir kap gibi.
9 Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
Tek başına dolaşan yaban eşeği gibi Asur'a gittiler, Efrayim ücretli oynaşlar tuttu.
10 Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
Uluslar arasında oynaşlar tutsalar da, Şimdi onları bir araya toplayacağım. Çünkü azalmaya başladılar güçlü kralın baskısı altında.
11 “Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
“Efrayim günah sunusu sunmak için çok sunak yaptı, Bunlar günah işlemelerine neden oldu.
12 Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
Yasamdaki pek çok şeyi onlar için yazdım, Ne var ki garipsediler bunları.
13 Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
Bana sundukları kurbanlara gelince, Kurban kesiyor, eti kendileri yiyorlar; Oysa RAB bunu yapanlardan hoşlanmaz. Şimdi anımsayacak suçlarını, Günahları için onları cezalandıracak; Geri dönecekler Mısır'a.
14 Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”
Çünkü İsrail Yaratıcısı'nı unuttu, Saraylar yaptı; Yahuda'ysa birçok kenti surlarla çevirdi, Ama ateş göndereceğim kentlerinin üstüne, Yiyip bitirsin kalelerini.”

< Hosiya 8 >