< Hosiya 8 >

1 “Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
Pon la trompeta en tu boca. Él viene como un águila contra la casa del Señor; porque han ido en contra de mi pacto, no han guardado mi ley.
2 Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
Clamarán a mi: Nosotros, Israel, te conocemos, oh Dios de Israel.
3 Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
Israel ha renunciado a lo que es bueno; Sus enemigos irán tras él.
4 Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
Han puesto reyes, pero no por mí; han nombrado príncipes, pero yo no lo sabía; han hecho imágenes de plata y oro, para su propia destrucción.
5 Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
No tendré nada que ver con tu becerro, oh Samaria; mi ira arde contra ellos; ¿Cuánto tiempo pasará antes de que los hijos de Israel se purifiquen?
6 Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
El artesano lo hizo, no es dios; El buey de Samaria se partirá en pedazos.
7 “Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
Porque han sembrado el viento, y su fruto será la tormenta; su grano no tiene tallo, no dará comida, y si lo tiene, una nación extranjera lo tomará.
8 An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
Israel ha venido a la destrucción; ahora están entre las naciones como una copa en la que no hay placer.
9 Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
Porque subieron a Asiria como un asno salvaje; Efraín ha comprado amantes.
10 Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
Pero aunque dan dinero a las naciones para que lo ayuden, los juntaré y los afligiré un poco por la carga del rey y gobernantes.
11 “Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
Debido a que Efraín ha aumentado los altares por el pecado, los altares se han convertido en una causa de pecado para él.
12 Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
Aunque pongo mi ley por escrito para él en diez mil reglas, son consideradas como algo extraño.
13 Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
Él da las ofrendas de sus amantes, y toma la carne como alimento; pero el Señor no tiene placer en ellos; ahora tendrá en cuenta su maldad y les dará el castigo de sus pecados; Regresarán a Egipto.
14 Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”
Porque Israel no tiene memoria de su Hacedor, y ha levantado los palacios de los reyes; y Judá ha hecho grande el número de sus ciudades amuralladas. Pero enviaré un incendio a sus pueblos y pondré fin a sus palacios.

< Hosiya 8 >