< Hosiya 8 >

1 “Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
Put the horn to your mouth! An eagle swoops down upon the house of the Lord because they have transgressed my covenant, trespassed against my law.
2 Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
To me they continually cry, “My God, we Israel, we know you!”
3 Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
But Israel has spurned that which is good, so let the foe pursue him.
4 Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
They themselves have made kings but without my consent. They have made princes but without my knowledge. Out of their silver and gold, they have made idols to their destruction!
5 Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
Your calf idol, O Samaria, is distasteful. My anger is kindled against them. How long will they escape punishment?
6 Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
Israel made the thing: a workman made it. It is not a god! Samaria’s calf will become mere splinters.
7 “Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
They sow the wind and will reap the whirlwind. A shoot which has no stalk, yields no fruit If it should yield, strangers would devour it.
8 An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
Israel is devoured. Already it lies discarded among the nations like a worthless pot.
9 Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
For by themselves they have gone up to Assyria like a wild donkey which wanders by itself. Ephraim pays for love
10 Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
but even if they sell themselves among the nations, I will round them up. Soon the kings and princes will writhe under the burden of tribute!
11 “Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
For as many altars as Ephraim has erected, they are to him altars for sinning,
12 Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
were I to write for him ever so many instructions, they would be regarded as from a stranger.
13 Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
The people love sacrifice, and so they offer sacrifices, meat, and so they eat it, although the Lord is not pleased with them, so now he will remember their guilt, and punish their sins. Back to Egypt with them!
14 Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”
For Israel forgot his Maker and built palaces, and Judah multiplied fortified cities. But I will send fire upon her cities, and it will devour her strongholds.

< Hosiya 8 >