< Hosiya 8 >

1 “Ka sa kakaki a leɓunanka! Gaggafa tana a bisan gidan Ubangiji domin mutane sun tā da alkawarina suka kuma tayar wa dokata.
Set the trumpet to thy mouth: he shall come as an eagle against the House of the Lord, because they haue transgressed my couenant, and trespassed against my Lawe.
2 Isra’ila ta yi mini kuka, ‘Ya Allahnmu, mun yarda da kai!’
Israel shall crie vnto me, My God, we know thee.
3 Amma Isra’ila sun ƙi abin da yake mai kyau; abokin gāba zai fafare su.
Israel hath cast off ye thing that is good: the enemie shall pursue him.
4 Suna naɗa sarakuna, ba da izinina ba; sun zaɓa shugabanni ba da yardanta ba. Da azurfa da zinariya sun ƙera gumaka wa kansu wanda zai kai zuwa ga hallakarsu.
They haue set vp a King, but not by me: they haue made princes, and I knew it not: of their siluer and their gold haue they made them idoles: therefore shall they be destroyed.
5 Ku zubar da gunkin maraƙinku, ya Samariya! Fushina yana ƙuna a kansu. Sai yaushe za su rabu da gumaka?
Thy calfe, O Samaria, hath cast thee off: mine anger is kindled against them: howe long will they be without innocencie!
6 Su daga Isra’ila ne! Wannan maraƙi, mai aikin hannu ne ya yi shi; gunki ne ba Allah ba. Za a farfashe shi kucu-kucu, waccan maraƙin Samariya.
For it came euen from Israel: the workeman made it, therefore it is not God: but the calfe of Samaria shall be broken in pieces.
7 “Gama sun shuka iska don haka za su girbe guguwa. Hatsin da yake tsaye ba shi da kai, ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci.
For they haue sowne the winde, and they shall reape the whirlewind: it hath no stalke: the budde shall bring foorth no meale: if so be it bring forth, the strangers shall deuoure it.
8 An haɗiye Isra’ila; yanzu tana cikin al’ummai kamar abin da ba shi da amfani.
Israel is deuoured, now shall they be among the Gentiles as a vessell wherein is no pleasure.
9 Gama sun haura zuwa Assuriya kamar jakin jejin da yake yawo shi kaɗai. Efraim ya sayar da kansa ga maza.
For they are gone vp to Asshur: they are as a wilde asse alone by himselfe: Ephraim hath hired louers.
10 Ko da yake sun sayar da kansu a cikin al’ummai, yanzu zan tattara su wuri ɗaya. Za su fara lalacewa a ƙarƙashi danniyar babban sarki.
Yet though they haue hired among the nations, nowe will I gather them, and they shall sorowe a litle, for the burden of the King and the princes.
11 “Ko da yake Efraim ya gina bagadai masu yawa don hadayun zunubi, waɗannan sun zama bagade don yin zunubi.
Because Ephraim hath made many altars to sinne, his altars shalbe to sinne.
12 Na rubuta musu abubuwa masu yawa na dokata, amma suka ɗauke su tamƙar wani baƙon abu ne.
I haue written to them the great things of my Lawe: but they were counted as a strange thing.
13 Suna miƙa hadayun da aka ba ni su kuma ci nama, amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Yanzu zai tuna da muguntarsu yă kuma hukunta zunubansu. Za su koma Masar.
They sacrifice flesh for ye sacrifices of mine offerings, and eate it: but the Lord accepteth them not: now will he remember their iniquitie, and visite their sinnes: they shall returne to Egypt.
14 Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”
For Israel hath forgotten his maker, and buildeth Temples, and Iudah hath increased strong cities: but I will sende a fire vpon his cities, and it shall deuoure the palaces thereof.

< Hosiya 8 >