< Hosiya 7 >
1 a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
Kad lijeèim Izrailja, tada se pokazuje bezakonje Jefremovo i zloæa Samarijska; jer èine laž, i lupež ulazi, i napolju udara èeta.
2 amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
I ne govore u srcu svom da ja pamtim svako bezakonje njihovo; sada stoje oko njih djela njihova, preda mnom su.
3 “Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
Nevaljalstvom svojim vesele cara i lažima svojim knezove.
4 Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
Svi èine preljubu; kao peæ su koju užari hljebar, koji prestane stražiti kad zamijesi tijesto pa dokle uskisne.
5 A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
Na dan cara našega razbolješe se knezovi od mijeha vina, i on pruži ruku svoju potsmjevaèima.
6 Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
Jer na zasjede svoje upravljaju srce svoje, koje je kao peæ; hljebar njihov spava cijelu noæ, ujutru gori kao plamen ognjeni.
7 Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
Svi su kao peæ ugrijani i proždiru svoje sudije; svi carevi njihovi padaju, nijedan izmeðu njih ne vièe k meni.
8 “Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
Jefrem se pomiješao s narodima; Jefrem je pogaèa neprevrnuta.
9 Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
Inostranci jedu mu silu, a on ne zna; sijede kose popadaju ga, a on ne zna.
10 Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
I ponositost Izrailjeva svjedoèi mu u oèi, ali se ne vraæaju ka Gospodu Bogu svojemu niti ga traže uza sve to.
11 “Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
I Jefrem je kao golub, lud, bezuman; zovu Misir, idu u Asirsku.
12 Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
Kad otidu, razapeæu na njih mrežu svoju, kao ptice nebeske svuæi æu ih, karaæu ih kako je kazivano u zboru njihovu.
13 Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
Teško njima, jer zaðoše od mene; pogibao æe im biti, jer me iznevjeriše; ja ih iskupih, a oni govoriše na me laž.
14 Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
Niti me prizivaše iz srca svojega, nego ridaše na odrima svojim; žita i vina radi skupljajuæi se otstupaju od mene.
15 Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
Kad ih karah, ukrijepih im mišice; ali oni misliše zlo na me.
16 Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.
Vraæaju se, ali ne k višnjemu, postaše kao luk lažljiv; knezovi æe njihovi popadati od maèa s obijesti jezika svojega; to æe im biti potsmijeh u zemlji Misirskoj.