< Hosiya 7 >
1 a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
Lorsque je voulais guérir Israël, l'iniquité d'Éphraïm et la méchanceté de Samarie se sont révélées; car ils ont pratiqué la fausseté; et tandis que le larron s'est introduit, la bande a pillé au-dehors. Et ils ne se disent pas, dans leurs cœurs, que je me souviens de toute leur malice.
2 amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
Maintenant leurs forfaits les environnent; ils sont devant ma face.
3 “Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
Ils réjouissent le roi par leur malice, et les chefs par leurs mensonges.
4 Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
Ils sont tous adultères, pareils au four chauffé par le boulanger, qui cesse d'attiser le feu depuis qu'il a pétri la pâte jusqu'à ce qu'elle soit levée.
5 A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
Au jour de notre roi, les chefs se rendent malades par l'ardeur du vin; le roi tend la main aux moqueurs.
6 Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
Lorsqu'ils dressent des embûches, leur cœur est un four; toute la nuit dort leur boulanger; au matin c'est un feu qui jette des flammes.
7 Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
Ils sont tous ardents comme un four, et ils dévorent leurs juges. Tous leurs rois tombent, et aucun d'eux ne crie à moi!
8 “Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
Éphraïm, lui, se mêle avec les peuples. Éphraïm est un gâteau qui n'a pas été retourné.
9 Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
Les étrangers ont dévoré sa force, et il ne l'a point senti; sa tête s'est parsemée de cheveux blancs, et il ne s'en est pas aperçu.
10 Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
Et l'orgueil d'Israël rend témoignage sur son visage: ils ne sont pas revenus à l'Éternel leur Dieu; ils ne l'ont point recherché, malgré tout cela.
11 “Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
Éphraïm est comme une colombe stupide, sans intelligence. Ils appellent l'Égypte, ils vont vers les Assyriens.
12 Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
Pendant qu'ils iront, j'étendrai sur eux mon filet; je les abattrai comme les oiseaux des cieux, je les châtierai, comme ils l'ont entendu dans leur assemblée.
13 Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
Malheur à eux! car ils me fuient. Ruine sur eux! car ils se rebellent contre moi. Moi, je les rachèterais; mais ils disent contre moi des mensonges.
14 Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
Ils ne crient pas du cœur vers moi, quand ils hurlent sur leurs couches. Ils s'inquiètent pour le froment et le vin; ils se détournent de moi.
15 Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
Je les ai châtiés; j'ai fortifié leurs bras; mais ils méditent du mal contre moi.
16 Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.
Ils retournent, mais non point au Souverain; ils sont comme un arc trompeur. Leurs chefs tomberont par l'épée, à cause de l'emportement de leur langue. Cela leur tournera en moquerie au pays d'Égypte.