< Hosiya 7 >

1 a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
When I would heal Israel, then is the iniquity of Ephraim discovered, and the wickedness of Samaria; for they commit falsehood: and the thief entereth in, [and] the troop of robbers spoileth without.
2 amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
And they consider not in their hearts that I remember all their wickedness: now have their own doings beset them about; they are before my face.
3 “Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
They make the king glad with their wickedness, and the princes with their lies.
4 Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
They are all adulterers; they are as an oven heated by the baker; he ceaseth to stir [the fire], from the kneading of the dough until it be leavened.
5 A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
On the day of our king the princes made themselves sick with the heat of wine; he stretched out his hand with scorners.
6 Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
For they have made ready their heart like an oven, whiles they lie in wait: their baker sleepeth all the night; in the morning it burneth as a flaming fire.
7 Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
They are all hot as an oven, and devour their judges; all their kings are fallen: there is none among them that calleth unto me.
8 “Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
Ephraim, he mixeth himself among the peoples; Ephraim is a cake not turned.
9 Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
Strangers have devoured his strength, and he knoweth [it] not: yea, gray hairs are here and there upon him, and he knoweth [it] not.
10 Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
And the pride of Israel doth testify to his face: yet they have not returned unto the LORD their God, nor sought him, for all this.
11 “Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
And Ephraim is like a silly dove, without understanding: they call unto Egypt, they go to Assyria.
12 Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
When they shall go, I will spread my net upon them; I will bring them down as the fowls of the heaven: I will chastise them, as their congregation hath heard.
13 Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
Woe unto them! for they have wandered from me; destruction unto them! for they have trespassed against me: though I would redeem them, yet they have spoken lies against me.
14 Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
And they have not cried unto me with their heart, but they howl upon their beds: they assemble themselves for corn and wine, they rebel against me.
15 Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
Though I have taught and strengthened their arms, yet do they imagine mischief against me.
16 Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.
They return, but not to [him that is] on high; they are like a deceitful bow: their princes shall fall by the sword for the rage of their tongue: this shall be their derision in the land of Egypt.

< Hosiya 7 >