< Hosiya 7 >

1 a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
When I was about to deliver my people from captivity, When I would have healed Israel, Then the iniquity of Ephraim was discovered, And the wickedness of Samaria; For they practise fraud, And the thief entereth in, And the band of robbers spoileth without.
2 amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
And they think not in their hearts, That I remember all their wickedness. Now shall their doings encompass them; They are before my face.
3 “Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
With their wickedness they gladden the king, And with their falsehoods the princes; All of them are adulterers;
4 Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
They are as an oven heated by the baker; He ceaseth to stir the fire, Until the dough which he hath kneaded be leavened.
5 A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
On the feast-day of our king, the princes are sick with the heat of wine, And he stretcheth out his hand with revilers.
6 Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
For they make ready their heart like an oven, while they lie in wait; All night the baker sleepeth; In the morning it gloweth like a flaming fire.
7 Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
They all glow as an oven; They have devoured their judges; All their kings have fallen; And none among them calleth upon me.
8 “Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
Ephraim hath mixed himself with the nations; Ephraim is a cake not turned.
9 Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
Strangers have devoured his strength, And he knoweth it not; Yea, gray hairs are sprinkled upon him, Yet he knoweth it not.
10 Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
The pride of Israel testifieth to his face; Yet do not they return to Jehovah their God, Nor seek him, for all this.
11 “Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
Ephraim is like a silly dove, without understanding; They call upon Egypt; they go to Assyria.
12 Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
When they go, I will spread my net over them; As birds of heaven will I bring them down. I will chastise them, as hath been proclaimed in their congregation.
13 Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
Woe to them, for they have wandered from me! Destruction upon them, for they have rebelled against me! Though I myself would redeem them, they speak falsely to me.
14 Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
They cry not to me from their heart, But howl upon their beds; For corn and wine they assemble themselves; They rebel against me.
15 Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
I have chastened them; I have also strengthened their arms; Yet do they devise evil against me.
16 Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.
They return, but not to the Most High; They are like a deceitful bow; Their princes shall fall by the sword for the haughtiness of their tongues; This shall be their reproach in the land of Egypt.

< Hosiya 7 >