< Hosiya 6 >
1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
“¡Ven! Volvamos a Yahvé; porque nos ha hecho pedazos, y nos curará; nos ha perjudicado, y vendará nuestras heridas.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Después de dos días nos revivirá. Al tercer día nos resucitará, y viviremos ante él.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
Reconozcamos a Yahvé. Sigamos adelante para conocer a Yahvé. Tan seguro como que sale el sol, Yahvé aparecerá. Vendrá a nosotros como la lluvia, como la lluvia de primavera que riega la tierra”.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
“Efraín, ¿qué voy a hacer contigo? Judá, ¿qué voy a hacer contigo? Porque tu amor es como una nube matutina, y como el rocío que desaparece pronto.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
Por eso los he despedazado con los profetas; Los maté con las palabras de mi boca. Sus juicios son como un relámpago.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Porque yo quiero misericordia y no sacrificio; y el conocimiento de Dios más que los holocaustos.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
Pero ellos, como Adán, han roto el pacto. Allí me fueron infieles.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Galaad es una ciudad de los que obran la iniquidad; está manchada de sangre.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Como las bandas de ladrones esperan para emboscar a un hombre, así que la compañía de sacerdotes asesina en el camino hacia Siquem, cometiendo crímenes vergonzosos.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
En la casa de Israel he visto una cosa horrible. Hay prostitución en Efraín. Israel está contaminado.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
“También, Judá, hay una cosecha señalada para ti, cuando restablezca la fortuna de mi pueblo.