< Hosiya 6 >

1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
Vinde, e tornemos ao Senhor, porque ele despedaçou, e nos sarará, feriu, e nos atará a ferida.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Depois de dois dias nos dará a vida: ao terceiro dia nos resuscitará, e viveremos diante dele.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
Então conheceremos, e proseguiremos em conhecer, ao Senhor: como a alva, está aparelhada a sua saída: e ele a nós virá como a chuva, como chuva serodia que rega a terra.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Que te farei, ó Ephraim? que te, farei, ó Judá? visto que a vossa beneficência é como a nuvem da manhã, e como o orvalho da madrugada, que passa.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
Por isso os cortei pelos profetas: pela palavras da minha boca os matei; e os teus juízos sairão como a luz.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Porque o que eu quero é a misericórdia, e não o sacrifício; e o conhecimento de Deus, mais do que os holocaustos.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
Porém eles traspassaram o concerto, como Adão; ali se portaram aleivosamente contra mim.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Gilead é uma cidade dos que obram iniquidade, calcada de sangue.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Como as tropas dos salteadores a alguns esperam, assim é a companhia dos sacerdotes; matam no caminho para Sichem, porque fazem abominações.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
Vejo uma coisa horrenda na casa de Israel: ali está a fornicação de Ephraim; Israel é contaminado.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Também para ti, ó Judá, foi assinada uma sega; quando eu tornar o cativeiro do meu povo.

< Hosiya 6 >