< Hosiya 6 >

1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
VENITE, e convertiamoci al Signore; perciocchè egli ha lacerato, ed altresì ci risanerà; egli ha percosso, altresì ci fascerà [le piaghe].
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Infra due giorni egli ci avrà rimessi in vita; nel terzo giorno egli ci avrà risuscitati, e noi viveremo nel suo cospetto.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
E conoscendo il Signore, proseguiremo a conoscerlo ancora; la sua uscita [sarà] stabilmente ordinata, come [quella del]l'alba; ed egli verrà a noi come la pioggia, come la pioggia della stagion della ricolta, [che] innaffia la terra.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Che ti farò, o Efraim? che ti farò, o Giuda? conciossiachè la vostra pietà [sia] simile ad una nuvola mattutina, ed alla rugiada, la qual viene la mattina, [e poi] se ne va via. Perciò, io [li] ho asciati per li profeti;
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
li ho uccisi per le parole della mia bocca; e i tuoi giudicii, [o Israele, ti sono stati pronunziati] al levar del sole.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Perciocchè io gradisco benignità, e non sacrificio; e il conoscere Iddio, anzi che olocausti.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
Ma essi hanno trasgredito il patto, come Adamo; ecco là, si son portati dislealmente inverso me.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Galaad [è] una città di operatori d'iniquità; è segnata di sangue.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
E come gli scherani aspettano gli uomini, così la compagnia de' sacerdoti uccide [le persone] in su la strada, verso Sichem; perciocchè han commesse scelleratezze.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
Io ho veduto nella casa d'Israele una cosa orribile; ivi [è] la fornicazione di Efraim, Israele si è contaminato.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Ancora porrà Giuda delle piante in te, quando io ritrarrò di cattività il mio popolo.

< Hosiya 6 >