< Hosiya 6 >

1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
Venez, [diront-ils], et retournons à l'Eternel, car c'est lui qui a déchiré, mais il nous guérira; il a frappé, mais il nous bandera [nos plaies.]
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Il nous aura remis en vie dans deux jours, et au troisième jour il nous aura rétablis, et nous vivrons en sa présence.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
Car nous connaîtrons l'Eternel, et nous continuerons à le connaître; son lever se prépare comme celui du point du jour, et il viendra à nous comme la pluie, comme la pluie de la dernière saison qui humecte la terre.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Que te ferai-je, Ephraïm? que te ferai-je, Juda? puisque votre piété est comme une nuée du matin, comme une rosée du matin qui s'en va.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
C'est pourquoi je les ai charpentés par mes Prophètes, je les ai tués par les paroles de ma bouche, et mes jugements sur eux seront [comme] la lumière qui se lève.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Car je prends plaisir à la miséricorde, et non point aux sacrifices; et à la connaissance de Dieu, plus qu'aux holocaustes.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
Mais ils ont transgressé l'alliance, comme [si elle eût été] d'un homme, en quoi ils se sont portés perfidement contre moi.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Galaad est une ville d'ouvriers d'iniquité, rusée à tuer.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Et comme les bandes des voleurs attendent quelqu'un, ainsi les Sacrificateurs, après avoir comploté, tuent les gens sur le chemin, du côté de Sichem; car ils exécutent leurs méchants desseins.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
J'ai vu une chose infâme dans la maison d'Israël; là est la prostitution d'Ephraïm, Israël en est souillé.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Aussi Juda te moissonnera, quand je ramènerai mon peuple captif.

< Hosiya 6 >