< Hosiya 6 >

1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
Venez, retournons à l’Éternel, car lui a déchiré, et il nous guérira; il a frappé, et il bandera nos plaies.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Dans deux jours, il nous fera vivre; au troisième jour, il nous mettra debout, et nous vivrons devant sa face,
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
et nous connaîtrons [et] nous nous attacherons à connaître l’Éternel. Sa sortie est préparée comme l’aube du jour; et il viendra à nous comme la pluie, comme la pluie de la dernière saison arrose la terre.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Que te ferai-je, Éphraïm? Que te ferai-je, Juda? Votre piété est comme la nuée du matin et comme la rosée qui s’en va de bonne heure.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
C’est pourquoi je les ai hachés par les prophètes, je les ai tués par les paroles de ma bouche… Et mon jugement sort comme la lumière.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Car j’ai aimé la bonté, et non le sacrifice, et la connaissance de Dieu plus que les holocaustes;
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
mais eux, comme Adam, ont transgressé [l’]alliance; là ils ont agi perfidement envers moi.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Galaad est une ville d’ouvriers d’iniquité, couverte de traces de sang.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Et comme les troupes [de voleurs] guettent un homme, la bande des sacrificateurs assassine sur le chemin de Sichem; car ils commettent des infamies.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
J’ai vu des choses horribles dans la maison d’Israël: là est la prostitution d’Éphraïm! Israël s’est souillé!
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Pour toi aussi, Juda, une moisson t’est assignée, quand je rétablirai les captifs de mon peuple.

< Hosiya 6 >