< Hosiya 6 >
1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
Venez et retournons à Yahweh;
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
car c’est lui qui a déchiré, il nous guérira; il frappe mais il bandera nos plaies.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
Après deux jours, il nous fera revivre; le troisième jour, il nous relèvera, et nous vivrons devant lui. Connaissons, appliquons-nous à connaître Yahweh; son lever est certain comme celui de l’aurore; et il viendra à nous comme l’ondée, comme la pluie tardive qui arrose la terre.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Que te ferai-je, Éphraïm? Que te ferai-je, Juda? Votre piété est comme une nuée du matin, comme la rosée matinale qui passe.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
C’est pourquoi je les ai taillés en pièces par les prophètes; je tes ai tués par les paroles de ma bouche; ton jugement, c’est la lumière qui se lèvera.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Car je prends plaisir à la piété, et non au sacrifice: à la connaissance de Dieu, plus qu’aux holocaustes.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
Mais, comme Adam, ils ont transgressé l’alliance; là, ils m’ont été infidèles.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Galaad est une ville de malfaiteurs, marquée de traces de sang.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Comme des bandits en embuscade, ainsi une troupe de prêtres assassine, sur la route de Sichem; car ils commettent la scélératesse.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
Dans la maison d’Israël j’ai vu des choses horribles; c’est là qu’Éphraïm se prostitue, qu’Israël s’est souillé.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Toi aussi, Juda, une moisson t’est destinée, quand je ramènerai la captivité de mon peuple.