< Hosiya 6 >

1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
Come so let us return to Yahweh for he he has torn to pieces and he will heal us he has struck and he will bind up us.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
He will restore to life us from two days on the day third he will raise up us and we may live before him.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
And let us know let us pursue to know Yahweh like [the] dawn [is] steadfast going forth his so he may come like the rain to us like [the] spring rain [which] it waters [the] land.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
What? will I do to you O Ephraim what? will I do to you O Judah and loyalty your [is] like a cloud of [the] morning and like dew rising early going.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
There-fore I will cut [them] in pieces by the prophets I will kill them by [the] words of mouth my and judgments your [is] light [which] it goes forth.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
For covenant loyalty I desire and not sacrifice and [the] knowledge of God more than burnt offerings.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
And they like Adam they have transgressed [the] covenant there they dealt treacherously with me.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Gilead [is] a town of doers of wickedness tracked from blood.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
And as wait for a person marauding bands an association of priests [the] way they murder Shechem towards for wickedness they have done.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
In [the] house of Israel I have seen (a horrible [thing] *Q(k)*) [is] there prostitution [belongs] to Ephraim it has made itself unclean Israel.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Also O Judah he has appointed a harvest for you when turn back I [the] captivity of people my.

< Hosiya 6 >