< Hosiya 6 >
1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
'Come, and let us return unto the LORD; for He hath torn, and He will heal us, He hath smitten, and He will bind us up.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
After two days will He revive us, on the third day He will raise us up, that we may live in His presence.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
And let us know, eagerly strive to know the LORD, His going forth is sure as the morning; and He shall come unto us as the rain, as the latter rain that watereth the earth.'
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
O Ephraim, what shall I do unto thee? O Judah, what shall I do unto thee? for your goodness is as a morning cloud, and as the dew that early passeth away.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
Therefore have I hewed them by the prophets, I have slain them by the words of My mouth; and thy judgment goeth forth as the light.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
For I desire mercy, and not sacrifice, and the knowledge of God rather than burnt-offerings.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
But they like men have transgressed the covenant; there have they dealt treacherously against Me.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Gilead is a city of them that work iniquity, it is covered with footprints of blood.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
And as troops of robbers wait for a man, so doth the company of priests; they murder in the way toward Shechem; yea, they commit enormity.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
In the house of Israel I have seen a horrible thing; there harlotry is found in Ephraim, Israel is defiled.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Also, O Judah, there is a harvest appointed for thee! When I would turn the captivity of My people,