< Hosiya 6 >
1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
»Kom, vi vil tilbage til HERREN! Han sønderrev, han vil og læge, han slog os, vil ogsaa forbinde.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Om to Dage gør han os levende, rejser os op den tredje; da lever vi for hans Aasyn.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
Saa lad os da kende, jage efter at kende HERREN! Som Morgenrøden er hans Opgang vis. Da kommer han til os som Regn, som Vaarregn, der væder Jorden.«
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Hvor kan jeg hjælpe dig, Efraim, hvor kan jeg hjælpe dig, Juda? Eders Kærlighed er Morgentaage, Dug, som aarle svinder!
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
Thi hugged jeg løs ved Profeter, dræbte med Ord af min Mund, min Ret straaler frem som Lys:
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Ej Slagtoffer — Kærlighed vil jeg, ej Brændofre — Kendskab til Gud!
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
De bryder Pagten i Adam, er mig utro der;
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Gilead er Udaadsmænds By, den er sølet i Blod.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Som en Stimandsflok er Præsternes Flok, de myrder paa Vejen til Sikem, gør Niddingsværk.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
Grufulde Ting har jeg set i Israels Hus, der har Efraim bolet, Israel blev uren.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Juda, ogsaa for dig er der fastsat en Høst, naar jeg vender mit Folks Skæbne, naar jeg læger Israel.