< Hosiya 6 >
1 “Ku zo, mu koma ga Ubangiji. Ya yayyage mu kucu-kucu amma zai warkar da mu; ya ji mana ciwo amma zai daure mana miyakunmu.
Kommer og lader os vende om til Herren; thi han har sønderrevet og vil læge os; har han slaget, vil han forbinde os.
2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu, a rana ta uku zai tashe mu, don mu rayu a gabansa.
Han skal gøre os levende efter to Dage; paa den tredje Dag skal han oprejse os, at vi maa leve for hans Ansigt.
3 Bari mu yarda da Ubangiji; bari mu nace gaba don mu yarda da shi. Muddin rana tana fitowa, zai bayyana; zai zo mana kamar ruwan bazara, kamar ruwan saman farko da yake jiƙe ƙasa.”
Og vi ville kende, jage efter at kende Herren, som Morgenrøden er hans Opgang vis; og han skal komme til os som Regnen, som Sildigregnen, der væder Jorden.
4 “Me zan yi da kai Efraim? Me zan yi da kai Yahuda? Ƙaunarku tana kamar hazon safiya, kamar raɓar safiya da takan ɓace.
Hvad skal jeg gøre ved dig, Efraim? hvad skal jeg gøre ved dig, Juda? da eders Kærlighed er som en Sky om Morgenen og som Duggen, der aarle gaar bort.
5 Saboda haka na yayyaga ku kucu-kucu tare da annabawana, na kashe ku da kalmomin bakina; hukuntaina sun haskaka kamar walƙiya a kanku.
Derfor huggede jeg bort ved Profeterne, ihjelslog dem ved min Munds Taler; og Dommene over dig komme for Lyset.
6 Gama jinƙai nake bukata, ba hadaya ba, ku kuma san Allah a maimakon hadayun ƙonawa.
Thi jeg har Lyst til Miskundhed og ikke til Offer og til Gudskundskab mer end Brændofre.
7 Kamar Adamu, sun tā da alkawari, sun yi mini rashin aminci a can.
Men de have overtraadt Pagten ligesom Adam; der ere de blevne troløse imod mig.
8 Gileyad birni ce ta mugayen mutane, da tabon alamun jini.
Gilead er en Misdæderstad, fuld af Blodspor.
9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, haka ƙungiyoyin firistoci suke; suna kisa a hanya zuwa Shekem, suna aikata laifofi bankunya.
Som en Stimand lurer, saaledes og en Flok Præster; de myrde paa Vejen til Sikem, thi skændige Ting have de begaaet.
10 Na ga wani abu mai bantsoro a gidan Isra’ila. A can Efraim ya miƙa wuya ga karuwanci Isra’ila kuma ta ƙazantu.
I Israels Hus har jeg set gruelige Ting; der har Efraim bedrevet Hor, Israel er besmittet.
11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuda, na shirya muku ranar girbi. “A duk sa’ad da zan mayar da dukiya wa mutanena,
Ogsaa Juda — over dig er bestemt en Høst, naar jeg omvender mit Folks Fangenskab.