< Hosiya 5 >
1 “Ku ji wannan, ku firistoci! Ku kasa kunne, ku Isra’ilawa! Ku saurara, ya ku gidan sarauta! Wannan hukunci yana a kanku, kun zama tarko a Mizfa, ragar da aka shimfiɗa a kan Tabor.
Слышите сия, жерцы, и вонмите, доме Израилев, и доме царев, внушите, понеже к вам есть суд: яко пругло бысте стражбе, и якоже мрежа распростерта на Итавирии,
2 ’Yan tawaye sun yi zurfi cikin kisan gilla. Zan hore su duka.
юже ловящии лов поткнуша, Аз же наказатель вам:
3 Na san Efraim ƙaf; Isra’ila ba a ɓoye take a gare ni ba. Efraim, yanzu ka juya ka shiga karuwanci; Isra’ila ta lalace.
Аз познах Ефрема, и Израиль не отступи от Мене, зане ныне соблуди Ефрем, и осквернися Израиль:
4 “Ayyukansu ba su ba su dama su koma ga Allahnsu ba. Halin karuwanci yana cikin zuciyarsu; ba su yarda da Ubangiji ba.
не положиша помышлений своих, еже возвратитися к Богу своему, яко дух блужения есть в них, и Господа не уведеша.
5 Girmankan Isra’ila yana ba da shaida a kansu; Isra’ilawa, har ma Efraim, sun yi tuntuɓe a cikin zunubinsu; Yahuda ma ya yi tuntuɓe tare da su.
И смирится укоризна Израилева в лице ему, и Израиль и Ефрем изнемогут в неправдах своих, изнеможет же и Иуда с ними.
6 Sa’ad da suka tafi tare da garkunan shanu, tumaki da awakinsu don su nemi Ubangiji, ba za su same shi ba; ya janye kansa daga gare su.
Со овцами и телцы пойдут взыскати Господа и не обрящут Его, уклонися бо от них.
7 Su marasa aminci ne ga Ubangiji; suna haihuwar shegu. Yanzu bukukkuwar Sabon Watansu za su cinye su da gonakinsu.
Яко Господа оставиша, яко чада чужда породиша себе: ныне пояст я ржа, и причастия их.
8 “Amon kakaki a Gibeya, ƙaho a Rama. Ku yi kirarin yaƙi a Bet-Awen; ku ja gaba, ya Benyamin.
Вострубите трубою на холмех, возгласите на высоких, проповедите в Дому Онове, ужасеся Вениамин,
9 Efraim za tă zama kango a ranar hukunci. A cikin kabilan Isra’ila na yi shelar abin da yake tabbatacce.
Ефрем в пагубу бысть во дни наказания: в племенех Израилевых показах верная.
10 Shugabannin Yahuda suna kamar waɗanda suke matsar da duwatsun shaidar da aka sa a kan iyaka ne. Zan zubo musu da fushina a kansu kamar rigyawar ruwa.
Быша князи Иудины яко прелагающе пределы: на ня излию яко воду гнев Мой.
11 An danne Efraim, an murƙushe ta a shari’a ta ƙudura ga bin gumaka.
Соодоле Ефрем соперника своего, попра суд, яко нача ходити вслед суетных.
12 Na zama kamar asu ga Efraim, kamar ruɓa ga mutanen Yahuda.
Аз же яко мятеж Ефремови и яко остен дому Иудину.
13 “Sa’ad da Efraim ya ga ciwonsa, Yahuda kuwa miyakunta, sai Efraim ya juya ga Assuriya, ya aika wurin babban sarki don neman taimako. Amma bai iya warkar da kai ba, bai iya warkar da miyakunka ba.
И виде Ефрем немощь свою и Иуда болезнь свою: и иде Ефрем ко Ассирием и посла послы ко царю Иариму: и той не возможе изцелити вас, и не престанет от вас болезнь.
14 Gama zan zama kamar zaki ga Efraim, kamar babban zaki ga Yahuda. Zan yage su kucu-kucu in tafi; zan kwashe su, ba wanda zai kuɓutar da su.
Зане Аз есмь яко панфирь Ефремови и яко лев дому Иудину: и Аз восхищу, и пойду, и возму, и не будет изимаяй:
15 Sa’an nan zan koma wurina sai sun yarda da laifinsu. Za su kuma nemi fuskata; cikin azabansu za su nace da nemana.”
пойду и возвращуся на место Свое, дондеже погибнут, и взыщут лица Моего.