< Hosiya 5 >

1 “Ku ji wannan, ku firistoci! Ku kasa kunne, ku Isra’ilawa! Ku saurara, ya ku gidan sarauta! Wannan hukunci yana a kanku, kun zama tarko a Mizfa, ragar da aka shimfiɗa a kan Tabor.
Preestis, here ye this, and the hous of Israel, perseyue ye, and the hous of the kyng, herkne ye; for whi doom is to you, for ye ben maad a snare to lokyng afer, and as a net spred abrood on Thabor.
2 ’Yan tawaye sun yi zurfi cikin kisan gilla. Zan hore su duka.
And ye bowiden doun sacrifices in to depthe; and Y am the lernere of alle hem.
3 Na san Efraim ƙaf; Isra’ila ba a ɓoye take a gare ni ba. Efraim, yanzu ka juya ka shiga karuwanci; Isra’ila ta lalace.
Y knowe Effraym, and Israel is not hid fro me; for now Effraym dide fornicacioun, Israel is defoulid.
4 “Ayyukansu ba su ba su dama su koma ga Allahnsu ba. Halin karuwanci yana cikin zuciyarsu; ba su yarda da Ubangiji ba.
Thei schulen not yiue her thouytis, that thei turne ayen to her God; for the spirit of fornicacioun is in the myddis of hem, and thei knewen not the Lord.
5 Girmankan Isra’ila yana ba da shaida a kansu; Isra’ilawa, har ma Efraim, sun yi tuntuɓe a cikin zunubinsu; Yahuda ma ya yi tuntuɓe tare da su.
And the boost of Israel schal answere in to the face therof, and Israel and Effraym schulen falle in her wickidnesse; also Judas schal falle with hem.
6 Sa’ad da suka tafi tare da garkunan shanu, tumaki da awakinsu don su nemi Ubangiji, ba za su same shi ba; ya janye kansa daga gare su.
In her flockis, and in her droues thei schulen go to seke the Lord, and thei schulen not fynde; he is takun awei fro hem.
7 Su marasa aminci ne ga Ubangiji; suna haihuwar shegu. Yanzu bukukkuwar Sabon Watansu za su cinye su da gonakinsu.
Thei trespassiden ayens the Lord, for thei gendriden alien sones; now the monethe schal deuoure hem with her partis.
8 “Amon kakaki a Gibeya, ƙaho a Rama. Ku yi kirarin yaƙi a Bet-Awen; ku ja gaba, ya Benyamin.
Sowne ye with a clarioun in Gabaa, with a trumpe in Rama; yelle ye in Bethauen, after thi bak, Beniamyn.
9 Efraim za tă zama kango a ranar hukunci. A cikin kabilan Isra’ila na yi shelar abin da yake tabbatacce.
Effraym schal be in to desolacioun, in the dai of amendyng, and in the lynagis of Israel Y schewide feith.
10 Shugabannin Yahuda suna kamar waɗanda suke matsar da duwatsun shaidar da aka sa a kan iyaka ne. Zan zubo musu da fushina a kansu kamar rigyawar ruwa.
The princes of Juda ben maad as takynge terme; Y schal schede out on hem my wraththe as watir.
11 An danne Efraim, an murƙushe ta a shari’a ta ƙudura ga bin gumaka.
Effraym suffrith fals chalenge, and is brokun bi doom; for he bigan to go after filthis.
12 Na zama kamar asu ga Efraim, kamar ruɓa ga mutanen Yahuda.
And Y am as a mouyte to Effraym, and as rot to the hous of Juda.
13 “Sa’ad da Efraim ya ga ciwonsa, Yahuda kuwa miyakunta, sai Efraim ya juya ga Assuriya, ya aika wurin babban sarki don neman taimako. Amma bai iya warkar da kai ba, bai iya warkar da miyakunka ba.
And Effraym siy his sikenesse, and Judas siy his boond. And Effraym yede to Assur, and sente to the kyng veniere. And he mai not saue you, nether he mai vnbynde the boond fro you.
14 Gama zan zama kamar zaki ga Efraim, kamar babban zaki ga Yahuda. Zan yage su kucu-kucu in tafi; zan kwashe su, ba wanda zai kuɓutar da su.
For Y am as a lionesse to Effraym, and as a whelp of a lioun to the hous of Juda.
15 Sa’an nan zan koma wurina sai sun yarda da laifinsu. Za su kuma nemi fuskata; cikin azabansu za su nace da nemana.”
Y my silf schal take, and go, and take awei, and noon is that schal delyuere. I schal go, and turne ayen to my place, til ye failen, and seken my face.

< Hosiya 5 >