< Hosiya 4 >

1 Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
Ey İsrailliler, dinleyin RAB'bin sözünü, Çünkü RAB'bin davası var bu ülkede yaşayanlarla; “Yok olmuş sevgi, sadakat, Tanrı bilgisi.
2 Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
Lanet, yalan, adam öldürme, hırsızlık, Zina almış her şeyin yerini. Zorbalık ediyorlar, Kan üstüne kan döküyorlar.
3 Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
Bu yüzden ülke yas tutuyor, Tükeniyor orada yaşayan herkes, Kırdaki hayvanlar, gökteki kuşlar Denizdeki balıklar...
4 “Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
“Ancak kimse kimseyle çekişmesin, Kimse kimseyi suçlamasın, Çünkü halkın kâhinle çekişenlere benziyor.
5 Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
Sen gündüz tökezleyeceksin, Peygamber de gece seninle birlikte, Yok edeceğim anneni.
6 mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
“Yok oldu halkım bilgisizlikten, Sen bilgiyi reddettiğin için, Ben de seni reddedeceğim, Bana kâhinlik etmeyesin diye. Sen Tanrın'ın yasasını unuttuğun için, Ben de senin çocuklarını unutacağım.
7 Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
Kâhinler çoğaldıkça Daha çok günah işlediler bana karşı, Onların onurunu utanca çevireceğim.
8 Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
Halkımın günahlarıyla besleniyorlar, Onların suç işlemesini istiyorlar.
9 Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
Halkın başına gelenler kâhinlerin başına da gelecek, Tuttukları yol yüzünden cezalandıracağım onları, Yaptıklarının karşılığını vereceğim.
10 “Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
Yiyecekler, ama doymayacaklar, Zina edecekler, ama çoğalmayacaklar. Çünkü RAB'bi dinlemekten vazgeçtiler.
11 ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
“Zina, yeni ve eski şarap insanın aklını başından alır.
12 Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
Halkım tahta puta danışıyor, Değneğinden yanıt alıyor. Çünkü zina ruhu onları saptırdı, Kendi Tanrıları'ndan ayrılarak zina ettiler.
13 Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
Dağ başlarında kurban kesiyor, Tepelerde meşe, aselbent, yabanıl fıstık ağaçları altında buhur yakıyorlar, Gölgeleri güzel olduğu için. Bu yüzden kızlarınız fahişelik ediyor, Gelinleriniz zina.
14 “Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
Fahişelik ettiklerinde kızlarınızı, Zina ettiklerinde gelinlerinizi cezalandırmayacağım. Çünkü erkekleriniz fahişelerle oynaşıyor, Putların tapınağında fuhuş yapanlarla kurban kesiyorlar. Anlayışsız halk mahvolacak.
15 “Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
“Ey İsrail, sen zina etsen de, Yahuda suç işlemese bari. “Gilgal'a gitmeyin, Beytaven'e çıkmayın. ‘Yaşayan RAB'bin hakkı için’ diye ant içmeyin.
16 Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
Çünkü İsrail inatçı bir inek gibi inat etti, Şimdi RAB nasıl güder onları otlakta kuzu gibi?
17 Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
Efrayim putlarına sarıldı, Bırak onu!
18 Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
İçkileri tükendi, Hâlâ zina ediyorlar; Önderleri rezilliğe gönül verdi.
19 Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
Rüzgar onları kanatlarına sardı, Kurbanları yüzünden utanacaklar.

< Hosiya 4 >