< Hosiya 4 >

1 Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
Poslušajte Gospodovo besedo, vi Izraelovi otroci, kajti Gospod ima polemiko s prebivalci dežele, zato ker tam ni resnice niti usmiljenja niti spoznanja Boga v deželi.
2 Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
S priseganjem, laganjem, ubijanjem, krajo in zagrešitvami zakonolomstva so izbruhnili in kri se dotika krvi.
3 Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
Zato bo dežela žalovala in kdor v njej prebiva bo opešal, z živalmi polja in s perjadjo neba. Da, tudi ribe morja bodo odvzete.
4 “Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
Vendarle naj se noben človek ne prepira niti naj ne graja drugega, kajti tvoje ljudstvo je kakor tisti, ki se prepirajo z duhovnikom.
5 Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
»Zato boš padel podnevi in tudi prerok bo padel s teboj ponoči in jaz bom uničil tvojo mater.
6 mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
Moje ljudstvo je uničeno zaradi pomanjkanja spoznanja. Ker si zavrnil spoznanje, bom tudi jaz zavrnil tebe, da mi ne boš duhovnik. Ker si pozabil postavo svojega Boga, bom tudi jaz pozabil tvoje otroke.
7 Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
Kakor so bili pomnoženi, tako so grešili zoper mene, zato bom njihovo slavo spremenil v sramoto.
8 Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
Jedo greh mojega ljudstva in svoja srca naravnavajo na svojo krivičnost.
9 Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
In tam bo, kakršno ljudstvo, takšen duhovnik, in jaz jih bom kaznoval za njihove poti in jim nagradil njihova početja.
10 “Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
Kajti jedli bodo, pa ne bodo imeli dovolj, zagrešili bodo vlačugarstvo, pa se ne bodo pomnožili, ker so opustili, da bi bili pozorni na Gospoda.
11 ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
Vlačugarstvo, vino in novo vino jemljejo srce.
12 Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
Moje ljudstvo sprašuje za nasvet pri svojih kladah in njihova palica jim napoveduje, kajti duh vlačugarstev jim je povzročil, da blodijo in odšli so se vlačugat proč izpred svojega Boga.
13 Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
Žrtvujejo na vrhovih gora in kadilo zažigajo na hribih, pod hrasti, topoli in bresti, ker je njihova senca dobra. Zatorej bodo vaše hčere zagrešile vlačugarstvo in vaše snahe bodo zagrešile zakonolomstvo.
14 “Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
Ne bom kaznoval vaših hčera, ko bodo zagrešile vlačuganje niti vaših snah, kadar bodo zagrešile zakonolomstvo, kajti oni sami so oddvojeni z vlačugami in žrtvujejo s pocestnicami. Zatorej bo ljudstvo, ki ne razume, padlo.
15 “Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
Čeprav ti, Izrael, igraš pocestnico, naj vendar Juda ne greši. Ne prihajajte v Gilgál, niti ne hodite gor v Bet Aven, niti ne prisegajte: › Gospod živi.‹
16 Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
Kajti Izrael drsi nazaj kakor nazaj zdrknjena telica. Sedaj jih bo Gospod pasel kakor jagnje na velikem kraju.
17 Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
Efrájim je pridružen malikom, pusti ga samega.
18 Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
Njihova pijača je kisla. Spet in spet zagrešujejo vlačugarstvo. Njegovi vladarji ljubijo s sramoto: ›Dajajte.‹
19 Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
Veter je [Izraela] zvezal v svoje peruti in osramočeni bodo zaradi svojih [klavnih] daritev.

< Hosiya 4 >