< Hosiya 4 >

1 Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
Слышите слово Господне, сынове Израилевы, яко суд Господеви к живущым на земли: зане несть истины, ни милости, ни ведения Божия на земли:
2 Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
клятва и лжа, и убийство и татьба и любодеяние разлияся по земли, и кровь с кровьми мешают.
3 Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
Сего ради восплачется земля и умалится со всеми вселившимися на ней, со зверьми польскими и с гады земными и со птицами небесными, и рыбы морския оскудеют:
4 “Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
яко да никтоже не прится, ни обличается никтоже: людие же мои аки пререкаемый жрец,
5 Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
и изнеможет во днех, и изнеможет пророк с тобою: нощи уподобих матерь твою.
6 mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
Уподобишася людие Мои аки не имуще умения: яко ты умение отвергл еси, отвергу и Аз тебе, еже не жречествовати Мне, и забыл еси закон Бога своего, забуду и Аз чада твоя.
7 Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
По множеству их тако согрешиша Мне: славу их в безчестие положу.
8 Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
Грехи людий Моих снедят и в неправдах их возмут душы их.
9 Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
И будет якоже людие, тако и жрец: и отмщу на них пути их, и умышления их воздам им.
10 “Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
И будут ясти и не насытятся: соблудиша и не исправятся: понеже Господа оставиша еже снабдети.
11 ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
Блуд и вино и пиянство прият сердце людий Моих.
12 Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
В знамениих вопрошаху и в жезлех своих поведаху тем: духом блужения прельстишася и соблудиша от Бога своего:
13 Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
на версех гор кадяху и на холмех жряху под дубом и под елию и под древом ветвенным, яко добр кров: сего ради соблудят дщери вашя, и невесты вашя возлюбодеют.
14 “Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
И не присещу на дщери вашя, егда соблудят, и на невесты вашя, егда возлюбодеют: яко и тии со блудницами смесишася и со блудниками требы жряху, и людие смыслящии со блудницею сплетахуся.
15 “Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
Ты же, Израилю, не не разумевай, и Иудо: не входите в Галгалу и не восходите в Дом Онов, и не кленитеся Господем живым.
16 Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
Зане якоже юница стрекалом стречема разсвирепе Израиль: ныне упасет я Господь, яко агнца на пространстве.
17 Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
Причастник кумиром Ефрем положи себе соблазны,
18 Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
избра Хананеов: блудяще возблудиша, возлюбиша безчестие от хрепетания своего.
19 Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
Вихр духа возсвищет в крилех своих, и посрамятся от требищ своих.

< Hosiya 4 >