< Hosiya 4 >
1 Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
Écoutez la parole du Seigneur, fils d’Israël, parce que voici venir le jugement du Seigneur avec les habitants de la terre; car il n’y a pas de vérité, et il n’y a pas de miséricorde, et il n’y a pas de science de Dieu sur la terre.
2 Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
L’imprécation, et le mensonge, et l’homicide, et le vol, et l’adultère, ont inondé la terre, et le sang s’est mêlé au sang.
3 Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
À cause de cela, la terre sera dans le deuil, et quiconque l’habite languira avec la bête de la campagne, et avec l’oiseau du ciel; et même les poissons de la mer seront enveloppés dans cette ruine.
4 “Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
Mais cependant que personne ne juge, et qu’aucun homme ne soit repris; car ton peuple est comme ceux qui contredisent le prêtre.
5 Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
Et tu succomberas aujourd’hui, et succombera aussi le prophète avec toi: la nuit j’ai réduit ta mère au silence.
6 mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
Mon peuple s’est tu à cause qu’il n’a pas eu la science; parce que toi, tu as rejeté la science, je te rejetterai, afin que tu n’exerces pas le sacerdoce pour moi; et comme tu as oublié la loi de ton Dieu, j’oublierai tes enfants, moi aussi.
7 Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
À proportion de leur multitude, ils ont péché contre moi; je changerai leur gloire en ignominie.
8 Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
Ils se nourriront des péchés de mon peuple, et ils encourageront leurs âmes dans leurs iniquités.
9 Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
Et comme sera le peuple, ainsi sera le prêtre; et je visiterai sur lui sa voie, et je lui rendrai selon ses pensées.
10 “Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
Et ils mangeront, et ils ne seront pas rassasiés; ils ont forniqué, et ils n’ont pas cessé, parce qu’ils ont abandonné le Seigneur en ne gardant point sa loi.
11 ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
La fornication, et le vin, et l’ivresse emportent le cœur.
12 Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
Mon peuple a interrogé son bois, et son bâton lui a annoncé l’avenir, car l’esprit de fornication les a déçus; et ils ont forniqué en se séparant de leur Dieu.
13 Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
Sur les sommets des montagnes ils sacrifiaient; et sur les collines ils brûlaient de l’encens; sous un chêne, et un peuplier, et un térébinthe, parce que bonne en était l’ombre; pour cela forniqueront vos filles, et vos femmes seront adultères.
14 “Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
Je ne punirai pas vos filles lorsqu’elles auront forniqué, ni vos femmes lorsqu’elles auront commis l’adultère; puisqu’eux mêmes vivaient avec des femmes de mauvaise vie, et qu’avec des efféminés ils sacrifiaient, et qu’un peuple non intelligent sera châtié.
15 “Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
Si tu forniques, toi, Israël, que Juda au moins ne pèche point, et n’entre pas à Galgala, et ne monte pas à Bethaven, et ne jure pas: Le Seigneur vit.
16 Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
Puisque, comme une génisse bondissante, Israël s’est détourné, maintenant le Seigneur les fera paître comme un agneau dans une vaste campagne.
17 Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
Ephraïm est attaché aux idoles; abandonne-le.
18 Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
Leur festin est séparé du vôtre; ils ont forniqué par la fornication; ses protecteurs ont aimé à le couvrir d’ignominie.
19 Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
Un vent l’a enveloppé dans ses ailes, et ils seront confondus par leurs sacrifices.