< Hosiya 4 >
1 Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
Écoutez la parole de Yahvé, enfants d'Israël, car Yahvé a une charge contre les habitants du pays: « En effet, il n'y a pas de vérité, ni de bonté, ni la connaissance de Dieu dans le pays.
2 Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
Il y a la malédiction, le mensonge, le meurtre, le vol et l'adultère; ils brisent les frontières, et les effusions de sang provoquent des effusions de sang.
3 Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
C'est pourquoi le pays sera dans le deuil, et tous ceux qui l'habitent dépériront, avec tous les êtres vivants en elle, même les animaux des champs et les oiseaux du ciel; oui, les poissons de la mer meurent aussi.
4 “Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
« Que personne ne porte plainte, que personne n'accuse; car ton peuple est comme ceux qui portent plainte contre un prêtre.
5 Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
Vous trébucherez le jour, et le prophète aussi trébuchera avec vous dans la nuit; et je détruirai ta mère.
6 mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
Mon peuple est détruit par manque de connaissance. Parce que vous avez rejeté la connaissance, je vous rejetterai aussi, pour que vous ne soyez pas un prêtre pour moi. Parce que vous avez oublié la loi de votre Dieu, J'oublierai aussi vos enfants.
7 Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
Comme ils se sont multipliés, ils ont péché contre moi. Je changerai leur gloire en honte.
8 Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
Ils se nourrissent du péché de mon peuple, et ont mis leur cœur dans leur iniquité.
9 Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
Il sera comme un peuple, comme un prêtre; et je les punirai pour leur conduite, et leur rendra la monnaie de leur pièce.
10 “Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
Ils mangeront, et n'auront pas assez. Ils joueront les prostituées, et n'augmenteront pas; parce qu'ils ont abandonné l'écoute de Yahvé.
11 ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
La prostitution, le vin et le vin nouveau enlèvent l'intelligence.
12 Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
Mon peuple consulte son idole de bois, et répondre à un bâton de bois. En effet, l'esprit de prostitution les a égarés, et ils ont été infidèles à leur Dieu.
13 Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
Ils sacrifient sur les sommets des montagnes, et brûlent de l'encens sur les collines, sous les chênes, les peupliers et les térébinthes, parce que sa teinte est bonne. C'est pourquoi vos filles jouent les prostituées, et vos épouses commettent l'adultère.
14 “Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
Je ne punirai pas vos filles lorsqu'elles se prostituent, ni vos épouses quand elles commettent l'adultère; parce que les hommes fréquentent des prostituées, et ils sacrifient avec les prostituées du sanctuaire; ainsi les gens sans compréhension viendront à la ruine.
15 “Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
« Bien que toi, Israël, tu joues les prostituées, mais ne laissez pas Judah s'offenser; et ne venez pas à Gilgal, ni aller jusqu'à Beth Aven, ni de jurer: « Comme Yahvé vit ».
16 Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
Car Israël s'est montré extrêmement têtu, comme une génisse obstinée. Alors comment Yahvé les nourrira-t-il comme un agneau dans une prairie?
17 Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
Ephraïm est attaché aux idoles. Laissez-le tranquille!
18 Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
Leur boisson est devenue aigre. Ils jouent continuellement la prostituée. Ses gouvernants aiment beaucoup leur manière honteuse.
19 Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
Le vent l'a enveloppée dans ses ailes; et ils seront déçus à cause de leurs sacrifices.