< Hosiya 4 >

1 Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
Hear the word of the LORD, ye children of Israel: for the LORD hath a controversy with the inhabitants of the land, because there is no truth, nor mercy, nor knowledge of God in the land.
2 Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
There is nought but swearing and breaking faith, and killing, and stealing, and committing adultery; they break out, and blood toucheth blood.
3 Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
Therefore shall the land mourn, and every one that dwelleth therein shall languish, with the beasts of the field and the fowls of heaven; yea, the fishes of the sea also shall be taken away.
4 “Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
Yet let no man strive, neither let any man reprove; for thy people are as they that strive with the priest.
5 Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
And thou shalt stumble in the day, and the prophet also shall stumble with thee in the night; and I will destroy thy mother.
6 mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
My people are destroyed for lack of knowledge: because thou hast rejected knowledge, I will also reject thee, that thou shalt be no priest to me: seeing thou hast forgotten the law of thy God, I also will forget thy children.
7 Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
As they were multiplied, so they sinned against me: I will change their glory into shame.
8 Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
They feed on the sin of my people, and set their heart on their iniquity.
9 Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
And it shall be, like people, like priest: and I will punish them for their ways, and will reward them their doings.
10 “Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
And they shall eat, and not have enough; they shall commit whoredom, and shall not increase: because they have left off to take heed to the LORD.
11 ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
Whoredom and wine and new wine take away the understanding.
12 Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
My people ask counsel at their stock, and their staff declareth unto them: for the spirit of whoredom hath caused them to err, and they have gone a whoring from under their God.
13 Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
They sacrifice upon the tops of the mountains, and burn incense upon the hills, under oaks and poplars and terebinths, because the shadow thereof is good: therefore your daughters commit whoredom, and your brides commit adultery.
14 “Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
I will not punish your daughters when they commit whoredom, nor your brides when they commit adultery; for they themselves go apart with whores, and they sacrifice with the harlots: and the people that doth not understand shall be overthrown.
15 “Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
Though thou, Israel, play the harlot, yet let not Judah offend; and come not ye unto Gilgal, neither go ye up to Beth-aven, nor swear, As the LORD liveth.
16 Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
For Israel hath behaved himself stubbornly, like a stubborn heifer: now will the LORD feed them as a lamb in a large place.
17 Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
Ephraim is joined to idols; let him alone.
18 Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
Their drink is become sour: they commit whoredom continually; her rulers dearly love shame.
19 Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
The wind hath wrapped her up in its wings; and they shall be ashamed because of their sacrifices.

< Hosiya 4 >