< Hosiya 4 >

1 Ku ji maganar Ubangiji, ku Isra’ilawa, gama Ubangiji yana da tuhumar da zai kawo a kan ku waɗanda suke zama a ƙasar. “Babu aminci, babu ƙauna, babu yarda da Allah a cikin ƙasar.
Hear the word of the Lord, ye children of Israel, for the Lord shall enter into judgment with the inhabitants of the land: for there is no truth, and there is no mercy, and there is no knowledge of God in the land.
2 Akwai la’ana ce kawai, yin ƙarya da kisa, yin sata da zina; sun wuce gona da iri, kisankai a kan kisankai.
Cursing, and lying, and killing, and theft, and adultery have overflowed, and blood hath touched blood.
3 Saboda wannan ƙasar tana makoki, kuma dukan waɗanda suke zama a cikinta sun lalace; namun jeji da tsuntsayen sararin sama da kuma kifin teku suna mutuwa.
Therefore shall the land mourn, and every one that dwelleth in it shall languish with the beasts of the field, and with the fowls of the air: yea, the fishes of the sea also shall be gathered together.
4 “Amma kada wani mutum yă kawo tuhuma, kada wani mutum yă zargi wani, gama mutanenka suna kama da waɗanda suke kawo tuhume-tuhume a kan firist ne.
But yet let not any man judge: and let not a man be rebuked: for thy people are as they that contradict the priest.
5 Kuna tuntuɓe dare da rana, annabawa ma suna tuntuɓe tare da ku. Saboda haka zan hallaka mahaifiyarku,
And thou shalt fall today, and the prophet also shall fall with thee: in the night I have made thy mother to be silent.
6 mutanena suna hallaka saboda jahilci. “Domin kun ƙi neman sani, ni ma na ƙi ku a matsayin firistocina; domin kun ƙyale dokar Allahnku, ni ma zan ƙyale’ya’yanku.
My people have been silent, because they had no knowledge: because thou hast rejected knowledge, I will reject thee, that thou shalt not do the office of priesthood to me: and thou hast forgotten the law of thy God, I also will forget thy children.
7 Yawan ƙaruwar firistoci, haka suke yawan zunubi a kaina; sun yi musaya Ɗaukakarsu da wani abin kunya.
According to the multitude of them so have they sinned against me: I will change their glory into shame.
8 Suna ciyar da kansu a kan zunuban mutanena suna kuma haɗamar muguntarsu.
They shall eat the sins of my people, and shall lift up their souls to their iniquity.
9 Zai kuwa zama, kamar yadda mutane suke, haka firistoci suke. Zan hukunta dukansu saboda al’amuransu in kuma sāka musu saboda ayyukansu.
And there shall be like people like priest: and I will visit their ways upon them, and I will repay them their devices.
10 “Za su ci amma ba za su ƙoshi ba; za su shiga karuwanci amma ba za su ƙaru ba, gama sun rabu da Ubangiji don su ba da kansu
And they shall eat and shall not be filled: they have committed fornication, and have not ceased: because they have forsaken the Lord in not observing his law.
11 ga karuwanci, ga tsoho da kuma sabon ruwan inabi, waɗanda suka ɗauke ganewar mutanena.
Fornication, and wine, and drunkenness take away the understanding.
12 Sun nemi shawarar gunkin da aka yi da itace suka kuwa sami amsa daga sanda. Halin karuwanci yakan ɓad da su; sun yi rashin aminci ga Allahnsu.
My people have consulted their stocks, and their staff hath declared unto them: for the spirit of fornication hath deceived them, and they have committed fornication against their God.
13 Suna miƙa hadaya a kan ƙwanƙolin duwatsu suna kuma ƙone hadayu a kan tuddai, a ƙarƙashin itatuwa oak, aduruku da katambiri, inda inuwa take da daɗi. Saboda haka’ya’yanku mata suka juya wa karuwanci surukanku mata kuma suka shiga yin zina.
They offered sacrifice upon the tops of the mountains, and burnt incense upon the hills: under the oak, and the poplar, and the turpentine tree, because the shadow thereof was good: therefore shall your daughters commit fornication, and your spouses shall be adulteresses.
14 “Ba zan hukunta’ya’yanku mata sa’ad da suka juya ga yin karuwanci ba, balle surukanku mata, sa’ad da suka yi zina, gama mazan da kansu suna ma’amala da karuwai suna kuma miƙa hadaya tare da karuwai na masujada, mutane marasa ganewa za su lalace!
I will not visit upon your daughters when they shell commit fornication, and upon your spouses when they shall commit adultery: because themselves conversed with harlots, and offered sacrifice with the effeminate, and the people that doth not understand shall be beaten.
15 “Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
If thou play the harlot, O Israel, at least let not Juda offend: and go ye not into Galgal, and come not up into Bethaven, and do not swear: The Lord liveth.
16 Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
For Israel hath gone astray like a wanton heifer: now will the Lord feed them, as a lamb in a spacious place.
17 Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
Ephraim is a partaker with idols, let him alone.
18 Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
Their banquet is separated, they have gone astray by fornication: they that should have protected them have loved to bring shame upon them.
19 Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
The wind hath bound them up in its wings, and they shall be confounded because of their sacrifices.

< Hosiya 4 >