< Hosiya 3 >

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
Potem mi je Gospod rekel: »Pojdi že, ljubi žensko, ljubljeno od njenega prijatelja, vendar zakonolomko, glede na Gospodovo ljubezen do Izraelovih otrok, ki gledajo k drugim bogovom in ljubijo flaškone vina.«
2 Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
Tako sem si jo kupil za petnajst koščkov srebra in za tovor ječmena in pol tovora ječmena.
3 Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
Rekel sem ji: »Mnogo dni boš čakala name. Ne boš igrala pocestnice in ne boš za drugega moškega; tako bom tudi jaz nate.«
4 Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
Kajti Izraelovi otroci bodo mnogo dni ostali brez kralja, brez princa, brez klavne daritve, brez podobe, brez efóda in brez družinskega malika.
5 Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.
Potem se bodo Izraelovi otroci vrnili in iskali Gospoda, svojega Boga in Davida, svojega kralja in bali se bodo Gospoda in njegove dobrote v zadnjih dneh.

< Hosiya 3 >