< Hosiya 3 >

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
Après cela l'Eternel me dit: Va encore aimer une femme aimée d'un [ami], et néanmoins adultère, selon l'amour de l'Eternel envers les enfants d'Israël, qui toutefois regardent à d'autres dieux, et aiment les flacons de vin.
2 Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
Je m'acquis donc cette [femme-]là pour quinze pièces d'argent et un homer et demi d'orge;
3 Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
Et je lui dis: Tu demeureras avec moi pendant plusieurs jours; tu ne t'abandonneras plus, et tu ne seras à aucun mari; et aussi je te serai fidèle.
4 Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
Car les enfants d'Israël demeureront plusieurs jours sans Roi et sans Gouverneur, sans sacrifice, et sans statue, sans Ephod et sans Théraphim.
5 Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.
Mais après cela les enfants d'Israël se repentiront, et rechercheront l'Eternel leur Dieu, et David leur Roi, ils révéreront l'Eternel et sa bonté aux derniers jours.

< Hosiya 3 >