< Hosiya 3 >

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
L’Eternel me dit encore: "Va derechef, accorde ton amour à une femme qui est aimée d’un autre et coupable d’adultère, tout comme Dieu aime les enfants d’Israël tandis qu’ils se tournent, eux, vers des dieux étrangers et raffolent de gâteaux de raisin.
2 Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
Je m’acquis cette femme pour quinze pièces d’argent, un homer plus un létec d’orge.
3 Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
Et je lui dis: "Tu me demeureras fidèle pendant de longs jours, sans te débaucher ni appartenir à aucun homme, de même en userai-je à ton égard."
4 Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
Car de longs jours, les enfants d’Israël demeureront isolés sans roi ni chef, sans sacrifice ni stèle, sans Ephod ni Pénates.
5 Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.
Après cela, les enfants d’Israël se remettront à rechercher l’Eternel, leur Dieu, et David, leur roi; ils accourront, le cœur ému, auprès de l’Eternel et de sa grâce, dans la suite des temps.

< Hosiya 3 >