< Hosiya 3 >
1 Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
And the LORD said unto me, Go yet, love a woman beloved of [her] friend and an adulteress, even as the LORD loveth the children of Israel, though they turn unto other gods, and love cakes of raisins.
2 Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
So I bought her to me for fifteen [pieces] of silver, and an homer of barley, and an half homer of barley:
3 Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
and I said unto her, Thou shalt abide for me many days; thou shalt not play the harlot, and thou shalt not be any man’s wife: so will I also be toward thee.
4 Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
For the children of Israel shall abide many days without king, and without prince, and without sacrifice, and without pillar, and without ephod or teraphim.
5 Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.
afterward shall the children of Israel return, and seek the LORD their God, and David their king; and shall come with fear unto the LORD and to his goodness in the latter days.