< Hosiya 3 >

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
Then said the Lord unto me, Go once more, love a woman beloved of her husband, yet committing adultery; like the love of the Lord toward the children of Israel, who turn themselves after other gods, and love flagons of wine.
2 Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
So I bought me such a one for fifteen pieces of silver, and for a chomer of barley, and half a chomer of barley.
3 Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
And I said unto her, Many days shalt thou abide [true] for me: thou shalt not play the harlot, and thou shalt not belong to any man, and so will I also be toward thee.
4 Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
For many days shall the children of Israel abide without a king, and without a prince, and without a sacrifice, and without a standing image, and without an ephod and theraphim.
5 Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.
After that will the children of Israel return, and seek for the Lord their God and David their king; and fearing will they hasten to the Lord and to his goodness in the latter days,

< Hosiya 3 >