< Hosiya 3 >

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi, ka sāke nuna wa matarka ƙauna, ko da yake wani yana son ta, ita kuma mazinaciya ce. Ka ƙaunace ta yadda Ubangiji yake ƙaunar Isra’ilawa, ko da yake sun juya ga waɗansu alloli suna kuma ƙauna wainar zabibi mai tsarki.”
And the Lord said to me: Go yet again, and love a woman beloved of her friend, and an adulteress: as the Lord loveth the children of Israel, and they look to strange gods, and love the husks of the grapes.
2 Ta haka na saye ta da shekel goma sha biyar na azurfa da kuma wajen buhu na sha’ir.
And I bought her to me for fifteen pieces of silver, and for a core of barley, and for half a core of barley.
3 Sai na faɗa mata, “Za ki zauna tare da ni kwanaki masu yawa; kada ki yi karuwanci ko ki yi abuta da wani namiji, ni kuwa zan zauna tare da ke.”
And I said to her: Thou shalt wait for me many days: thou shalt not play the harlot, and thou shalt be no man’s, and I also will wait for thee.
4 Gama Isra’ilawa za su yi kwanaki masu yawa ba tare da sarki ko shugaba ba, babu hadaya ko keɓaɓɓun duwatsu, babu efod ko gunki.
For the children of Israel shall sit many days without king, and without prince, and without sacrifice, and without altar, and without ephod, and without theraphim.
5 Daga baya Isra’ilawa za su dawo su nemi Ubangiji Allahnsu da kuma Dawuda sarkinsu. Za su je da rawan jiki wajen Ubangiji da kuma ga albarkunsa a kwanakin ƙarshe.
And after this the children of Israel shall return, and shall seek the Lord their God, and David their king: and they shall fear the Lord, and his goodness in the last days.

< Hosiya 3 >