< Hosiya 2 >
1 “Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
Dizei a vossos irmãos, ami, e a vossas irmãs, Ruhama:
2 “Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
Contendei com vossa mãe, contendei, porque ela não é minha mulher, e eu não sou seu marido, e tire ela as suas fornicações da sua face e os seus adultérios de entre os seus peitos.
3 In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
Para que eu não a despoje despida, e a ponha como no dia em que nasceu, e a faça como um deserto, e a ponha como uma terra seca, e a mate à sede,
4 Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
E não me apiede de seus filhos, porque são filhos de fornicações.
5 Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
Porque sua mãe fornicou: aquela que os concebeu houve-se torpemente, porque diz: Irei atráz de meus namorados, que me dão o meu pão e a minha água, a minha lã e o meu linho, o meu óleo e as minhas bebidas.
6 Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
Portanto, eis que cercarei o teu caminho com espinhos; e levantarei uma parede de sebe, e não achará as suas veredas.
7 Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
E irá em seguimento de seus amantes, mas não os alcançará; e busca-los-á, mas não os achará: então dirá: ir-me-ei, e tornar-me-ei a meu primeiro marido, porque melhor me ia então do que agora.
8 Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
Ela pois não reconhece que eu lhe dei o grão, e o mosto, e o óleo, e lhe multipliquei a prata e o ouro, do que usaram para Baal.
9 “Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
Portanto, tornar-me-ei, e a seu tempo tirarei o meu grão e o meu mosto ao seu determinado tempo; e arrebatarei a minha lã e o meu linho, que tinha dado para cobrir a sua nudez.
10 Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
E agora descobrirei a sua vileza diante dos olhos dos seus namorados, e ninguém a livrará da minha mão.
11 Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
E farei cessar todo o seu gozo, as suas festas, as suas luas novas, e os seus sábados, e todas as suas festividades.
12 Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
E assolarei a sua vide e a sua figueira, de que ela diz: Estas são a minha paga que me deram os meus amantes: eu pois farei delas um bosque, e as bestas feras do campo as devorarão.
13 Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
E sobre ela visitarei os dias de Baal, em que lhe queimou incenso, e se adornou dos seus pendentes e das suas gargantilhas, e andou atráz de seus namorados, mas de mim se esqueceu, diz o Senhor.
14 “Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
Portanto, eis que eu a atrairei, e a levarei para o deserto, e lhe falarei ao coração.
15 A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
E lhe darei as suas vinhas dali, e o vale de Achor, para porta de esperança; e ali cantará, como nos dias da sua mocidade, e como no dia em que subiu da terra do Egito.
16 “A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
E será naquele dia, diz o Senhor, que me chamarás: Meu marido; e não me chamarás mais: Meu Baal.
17 Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
E da sua boca tirarei os nomes de Baalim, e os seus nomes não virão mais em memória.
18 A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
E naquele dia lhes farei aliança com as bestas feras do campo, e com as aves do céu, e com os réptis da terra; e da terra quebrarei o arco, e a espada, e a guerra, e os farei deitar em segurança.
19 Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
E desposar-te-ei comigo para sempre: desposar-te-ei comigo em justiça, e em juízo, e em benignidade, e em misericórdias.
20 Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
E desposar-te-ei comigo em fidelidade, e conhecerás ao Senhor.
21 “A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
E acontecerá naquele dia que eu responderei, diz o Senhor, eu responderei aos céus, e estes responderão à terra.
22 ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
E a terra ouvirá ao trigo, como também ao mosto, e ao óleo, e estes responderão a Jezreel.
23 Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”
E semea-la-ei para mim na terra, e apiedar-me-ei de Lo-ruhama; e a lo-ami direi: Tu és meu povo; e ele dirá: Ó meu Deus!