< Hosiya 2 >

1 “Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
Dites à vos frères: Mon peuple; et à votre sœur: Tu as reçu miséricorde.
2 “Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
Jugez votre mère, jugez-la; elle n’est pas mon épouse, et moi je ne suis pas son époux; qu’elle ôte ses fornications de sa face, et ses adultères du milieu de son sein.
3 In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
De peur que je ne la dépouille à nu, et que je ne la mette comme au jour de sa naissance; et que je ne la réduise en solitude, et que je ne la rende comme une terre inaccessible, et que je ne la fasse mourir de soif.
4 Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
Je n’aurai pas pitié de ses enfants, parce que ce sont des enfants de fornications:
5 Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
Parce que leur mère a forniqué, que celle qui les a conçus s’est couverte de confusion; parce qu’elle a dit: J’irai après mes amants, qui me donnent mon pain et mon eau, ma laine et mon lin, mon huile et mon breuvage.
6 Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
À cause de cela, voici que moi, j’entourerai ton chemin d’une haie d’épines, je l’entourerai d’une muraille, et elle ne retrouvera pas ses sentiers.
7 Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
Et elle poursuivra ses amants, et elle ne les atteindra pas; et elle les cherchera, et elle ne les trouvera pas; et elle dira: J’irai, et je retournerai à mon premier mari, parce que j’étais alors mieux que maintenant.
8 Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
Elle n’a pas su que moi, je lui ai donné le blé, le vin et l’huile; j’ai multiplié pour elle l’argent et l’or qui ont fait Baal.
9 “Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
C’est pour cela que je changerai, et que je reprendrai mon blé en son temps et mon vin en son temps; et que j’enlèverai mon lin et ma laine qui couvraient son ignominie.
10 Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
Et maintenant je révélerai sa folie aux yeux de ses amants, et pas un homme ne l’arrachera de ma main.
11 Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
Et je ferai cesser sa joie, ses solennités, ses néoménies, son sabbat et tous ses temps de fêtes.
12 Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
Je gâterai sa vigne et son figuier dont elle disait: Ce sont mes récompenses que m’ont données mes amants; et j’en ferai une forêt, et la bête de la campagne la mangera.
13 Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
Et je visiterai sur elle les jours de Baalim, pendant lesquels elle brûlait de l’encens, et se parait de ses pendants d’oreilles et de son collier, et allait après ses amants, et m’oubliait, dit le Seigneur.
14 “Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
À cause de cela, voici que moi, je l’attirerai doucement et l’amènerai dans la solitude, et je parlerai à son cœur.
15 A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
Et je lui donnerai des vignerons du même lieu, et la vallée d’Achor pour lui ouvrir une espérance; et elle chantera là comme aux jours de sa jeunesse, et comme au jour où elle remonta de la terre d’Egypte.
16 “A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
Et il arrivera qu’en ce jour-là, dit le Seigneur, elle m’appellera: Mon époux, et elle ne m’appellera plus Baali.
17 Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
J’ôterai de sa bouche les noms de Baalim, et elle ne se souviendra plus de leur nom.
18 A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
Et je contracterai en ce jour-là une alliance avec eux, avec la bête de la campagne, et avec l’oiseau du ciel, et avec le reptile de la terre; et je briserai l’arc, et le glaive, et la guerre, en les faisant disparaître de la terre, et je les ferai dormir dans la confiance.
19 Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
Et je te prendrai pour mon épouse à jamais: et je te prendrai pour mon épouse par la justice, et par le jugement, et par la miséricorde, et par les bontés.
20 Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
Et je te prendrai pour mon épouse par la foi, et tu sauras que je suis le Seigneur.
21 “A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
Et il arrivera qu’en ce jour-là, j’exaucerai, dit le Seigneur, j’exaucerai les cieux, et eux exauceront la terre.
22 ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
Et la terre exaucera le blé, et le vin, et l’huile, et ces choses exauceront Jezrahel.
23 Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”
Je la sèmerai sur la terre, et j’aurai pitié de celle qui fut nommée Sans miséricorde. Et je dirai à celui qui n’était pas mon peuple: Tu es mon peuple; et lui dira: Vous êtes mon Dieu, vous.

< Hosiya 2 >