< Hosiya 2 >
1 “Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
Call ye your brethren My-people; and your sisters Pitied.
2 “Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
Contend ye with your mother, contend! For she is not my wife, Nor am I her husband; That she put away lewdness from her face, And adultery from her breasts, Lest I strip her naked, And expose her, as when she was born;
3 In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
Lest I make her as the desert, and like a parched land, And kill her with thirst.
4 Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
Upon her sons also I will not have pity, For they are the sons of lewdness.
5 Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
For their mother hath been guilty of lewdness; She that bore them hath brought upon herself shame; For she said, I will go after my lovers, Who give me my food and my water, My wool and my flax, my oil and my strong drink.
6 Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
Therefore, behold, I will hedge up her way with thorns, And I will enclose her with a wall, So that she shall not find her paths.
7 Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
When she followeth after her lovers, she shall not overtake them; When she seeketh them, she shall not find them. Then shall she say, I will go back to my former husband, For then it was better with me than now.
8 Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
For she did not consider that I gave her corn, and wine, and oil, And multiplied silver unto her, And gold, of which they made images of Baal.
9 “Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
Therefore will I take back my corn in its time, And my new wine in its season, And I will take away my wool and my flax, Which covered her nakedness.
10 Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
And now will I reveal her shame before the eyes of her lovers, And none shall deliver her out of my hand.
11 Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
And I will cause all her joy to cease; Her feasts, and new moons, and sabbaths, And all her festal days.
12 Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
I will destroy her vines, and her fig-trees, Of which she said, These are my hire, Which my lovers have given me; And I will make them a forest, And the wild beasts shall eat them.
13 Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
I will punish her for the days of the Baals, When she burned incense to them, And decked herself with her rings and her jewels, And went after her lovers, And forgot me, saith Jehovah.
14 “Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
Therefore, behold, I will allure her, And will lead her to the desert, And will speak kindly to her;
15 A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
And thence will I give her her vineyards, And the valley of Achor for a door of hope; And there shall she sing, as in the days of her youth! As in the day when she came up from the land of Egypt.
16 “A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
At that time, saith Jehovah, Thou shalt call me, MY HUSBAND; Thou shalt no more call me, MY BAAL;
17 Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
For I will take away the name of the Baals out of her mouth, And their name shall no more be uttered.
18 A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
At that time will I make for them a covenant With the beasts of the forest, and with the birds of heaven, And with the creeping things of the ground. The bow and the sword and the battle will I break from the land, And I will cause them to lie down in safety.
19 Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
I will betroth thee to me forever; Yea, I will betroth thee to me in righteousness, and in justice, And in kindness, and in tender love.
20 Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
Yea, I will betroth thee to me in faithfulness, And thou shalt know Jehovah.
21 “A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
At that time will I hear, saith Jehovah; I will hear the heavens; And they shall hear the earth,
22 ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
And the earth shall hear the corn, and the new wine, and the oil, And they shall hear Jezreel.
23 Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”
And I will plant her for myself in the land; And I will have pity upon her that was called Unpitied; And I will say to them called Not-my-people, Thou art my people; And they shall say, Thou art my God.