< Hosiya 2 >
1 “Ka ce da’yan’uwanka maza, ‘Mutanena,’ ka kuma ce da’yan’uwanka mata, ‘Ƙaunatacciyata.’
Say to your brother, My people, and to your sister, Pitied.
2 “Ka tsawata wa mahaifiyarka, ka tsawata mata, gama ita ba matata ba ce, ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta tă daina karuwancinta da kuma rashin aminci a tsakanin nononta.
Plead with your mother, plead: for she is not my wife, and I am not her husband: and I will remove her fornication out of my presence, and her adultery from between her breasts:
3 In ba haka ba zai tuɓe ta tsirara in bar ta kamar yadda take a ranar da aka haife ta; zan sa ta zama kamar hamada, in mayar da ita busasshiyar ƙasar, in kashe ta da ƙishirwa.
that I may strip her naked, and make her again as she was at the day of her birth: and I will make her desolate, and make her as a dry land, and will kill her with thirst.
4 Ba zan nuna wa’ya’yanta ƙaunata ba, domin su’ya’yan zina ne.
And I will not have mercy upon her children; for they are children of fornication.
5 Mahaifiyarsu ta yi rashin aminci ta kuma ɗauki cikinsu ta wurin yi abin kunya. Ta ce, ‘Zan bi kwartayena, waɗanda suke ba ni abinci da ruwa, ulu nawa da lilina, mai nawa da kuma abin sha na.’
And their mother went a-whoring: she that bore them disgraced [them]: for she said, I will go after my lovers, that give me my bread and my water, and my garments, and my linen clothes, my oil and my necessaries.
6 Saboda haka zai tare hanyarta da ƙaya; zan yi mata katanga don kada tă sami hanya.
Therefore, behold, I hedge up her way with thorns, and I will stop the ways, and she shall not find her path.
7 Za tă bi kwartayenta amma ba za tă kama su ba; za tă neme su amma ba za tă same su ba. Sa’an nan za tă ce, ‘Zan koma ga mijina na fari, gama dā ya fi mini yadda nake a yanzu.’
And she shall follow after her lovers, and shall not overtake them; and she shall seek them, but shall not find them: and she shall say, I will go, and return to my former husband; for it was better with me than now.
8 Ba ta yarda cewa ni ne wanda ya ba ta hatsi, sabon ruwan inabi da mai ba, wanda ya jibge mata azurfa da zinariya, waɗanda suka yi amfani wa Ba’al ba.
And she knew not that I gave her her corn, and wine, and oil, and multiplied silver to her: but she made silver and gold [images] for Baal.
9 “Saboda haka zan ƙwace hatsina sa’ad da ya nuna, da sabon ruwan inabina sa’ad da ya ƙosa. Zan karɓe ulu nawa da lilina, da take niyya ta rufe tsiraicinta.
Therefore I will return, and take away my corn in its season, and my wine in its time; and I will take away my raiment and my linen clothes, so that she shall not cover her nakedness.
10 Saboda haka yanzu zan buɗe tsiraicinta a idanun kwartayenta; ba wani da zai ƙwace ta daga hannuwana.
And now I will expose her uncleanness before her lovers, and no one shall by any means deliver her out of my hand.
11 Zan tsayar da dukan bukukkuwarta, bukukkuwarta na shekara-shekara, da kuma kiyaye bikin Sababbin Wata nata, kwanakin Asabbacinta, dukan ƙayyadaddun bukukkuwarta.
And I will take away all her gladness, her feasts, and her festivals at the new moon, and her sabbaths, and all her solemn assemblies.
12 Zan lalatar da inabinta da kuma itatuwan ɓaurenta, waɗanda take cewa su ne abin da kwartayenta suka biya; zan mayar da su kurmi, namun jeji kuwa za su ci su.
And I will utterly destroy her vines, and her fig-trees, all things of which she said, These are my hire which my lovers have given me: and I will make them a testimony, and the wild beasts of the field, and the birds of the sky, and the reptiles of the earth shall devour them.
13 Zan hukunta ta saboda kwanakin da ta ƙone turare wa Ba’al; ta yi wa kanta ado da zobai da duwatsu masu daraja, ta bi kwartayenta, amma ta manta da ni,” in ji Ubangiji.
And I will recompense on her the days of Baalim, wherein she sacrificed to them, and put on her ear-rings, and her necklaces, and went after her lovers, and forgot me, saith the Lord.
14 “Saboda haka yanzu zan rarrashe ta; zan bishe ta zuwa hamada in kuma yi mata magana a hankali.
Therefore, behold, I [will] cause her to err, and will make her as desolate, and will speak comfortably to her.
15 A can zan mayar mata da gonakin inabinta, zan kuma sa Kwarin Akor yă zama ƙofar bege. A can za tă rera kamar a kwanakin ƙuruciyarta, kamar a lokacin da ta fita daga Masar.
And I will giver her possessions from thence, and the valley of Achor to open her understanding: and she shall be afflicted there according to the days of her infancy, and according to the days of her coming up out of the land of Egypt.
16 “A waccan rana,” in ji Ubangiji, “za ki ce da ni ‘mijina’; ba za ki ƙara ce ni ‘maigidana’ ba.
And it shall come to pass in that day, saith the Lord, [that] she shall call me, My husband, and shall no longer call me Baalim.
17 Zan cire sunayen Ba’al daga leɓunanta; ba za a ƙara kira sunayensu ba.
And I will take away the names of Baalim out of her mouth, and their names shall be remembered no more at all.
18 A waccan rana zan yi alkawari dominsu da namun jeji da kuma tsuntsayen sararin sama da dukan halittu masu rarrafe a ƙasa. Baka da takobi da yaƙi zan sa su ƙare a ƙasar, domin duk su zauna lafiya.
And I will make for them in that day a covenant with the wild beasts of the field, and with the birds of the sky, and with the reptiles of the earth: and I will break the bow and the sword and the battle from off the earth, and will cause thee to dwell safely.
19 Zan ɗaura aure da ke har abada; zan ɗaura aure da yake cikin adalci da gaskiya, cikin ƙauna da jinƙai.
And I will betroth thee to myself for ever; yea, I will betroth thee to myself in righteousness, and in judgment, and in mercy, and in tender compassions;
20 Zan ɗaura aure da yake cikin aminci za ki kuwa yarda cewa ni ne Ubangiji.
and I will betroth thee to myself in faithfulness: and thou shalt know the Lord.
21 “A waccan rana zan amsa,” in ji Ubangiji, “zan amsa wa sararin sama, za su kuwa amsa wa ƙasa;
And it shall come to pass in that day, saith the Lord, I will hearken to the heaven, and it shall hearken to the earth;
22 ƙasa kuma za tă amsa wa hatsi, sabon ruwan inabi da kuma mai, su kuma za su amsa wa Yezireyel.
and the earth shall hearken to the corn, and the wine, and the oil; and they shall hearken to Jezrael.
23 Zan dasa ta wa kaina a ƙasar; zan shuka ƙaunata ga wanda na ce ‘Ba ƙaunatacciyata ba.’ Zan faɗa wa waɗanda a ce ‘Ba mutanena ba,’ ‘Ku mutanena ne’; za su kuwa ce, ‘Kai ne Allahna.’”
And I will sow her to me on the earth; and will love her that was not loved, and will say to that which was not my people, Thou art my people; and they shall say, Thou art the Lord my God.